Posts

Showing posts with the label Buda Baki

Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Gudanar Da Taron Shan Ruwa Na Mutum Dubu Biyu

Image
Zababben Dan majalisar  tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Kiru da Bebeji, Abdulmumin Jibrin Kofa (Jarman Bebeji) ya jagoranci taron shan ruwa da al'umar Kiru da Bebeji mutane 2000 a gidansa dake garin Kofa. Bayan buda baki Kofa ya jagoranci mahalatta wannan taro Sallah.  Taron shan ruwan ya sami halartar Dagatai, Limamai, 'Yan siyasa, da sauran mutane daban-daban dake mazabarsa ta dan majalisar tarayya  Yayin taron, anyi amfani da wannan dama wajen yi wa Zababben Dan Majalisar Tarayyar, Alhaji Abdulmumin Jibrin Kofa addu'a da  Gwamna jihar Kano mai jiran rantsuwa Injiniya Abba Kabir . Yusif tare da Jagoran Kwankwasiyya Sanata Rabiu Musa Kwankwaso. Haka kuma an roki madaukakin Sarki Allah ya dauwamar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Jahar Kano da ma Najeriya baki daya