Posts

Showing posts with the label Yajin aiki

Labari da dumiduminsa: Kungiyar Kwadago ta janye yajin aikin da ta fara gudanarwa

Image
Kungiyar Kwadagon ta kasa ta Janye yajin aikin ne bayan zaman tattaunawar da mai bawa Shugaban kasa shawara kan harkokin tsaro, Malam Nuhu Ribadu Cikakken labarin zai zo muku nan gaba 

Kungiyar Kwadago Za Ta Fara Yajin Aikin Sai Baba Ta Gani Daga Gobe Talata

Image
Kungiyar Kwadago ta Najeriya da kungiyar ‘yan kasuwa ta Najeriya sun umurci mambobin kungiyar da su shiga yajin aikin gama gari daga tsakar daren ranar 14 ga Nuwamba, 2023. Shugaban kungiyar ta TUC, Festus Osifo ne ya bayyana haka yayin da yake jawabi ga manema labarai a Abuja ranar Litinin. Osifo ya ce yajin aikin zai ci gaba da kasancewa har sai “gwamnati a dukkan matakai sun farga da alhakin da ya rataya a wuyansu.” Har ila yau yajin aikin na zanga-zangar ne don nuna rashin amincewa da yadda aka yi wa shugaban NLC, Joe Ajaero, da wasu shugabannin majalisar suka yi a Owerri, jihar Imo, a ranar 1 ga watan Nuwamba, da kuma matsalolin da ke addabar ma’aikata a jihar Imo. ‘Yan sanda sun kama Ajaero ne gabanin wata zanga-zangar da aka yi a jihar Imo, kamar yadda shugaban yada labarai na NLC, Benson Upah ya bayyana. Ko da yake rundunar ‘yan sandan ta musanta kama Ajaero, inda ta bayyana cewa an tsare shi ne kawai don kare kai harin, gwamnan jihar Imo, Hope Uzodimma, ya zargi sh

Likitocin Najeriya Sun Fara Gudanar Da Yajin Aikin Gama-Gari

Image
Likitoci Masu Neman Kwarewa a fadin Najeriya sun fara yajin aikin sai abin da hali ya yi daga safiyar nan ta Laraba. Kungiyar likitocin (NARD) ta sanar da shiga yajin aikin ne jim kadan bayan zaman Majalisar Zartarwarta da ya gudana a Legas a ranar Talata. Shugaban kungiyar, Dokta Orji Emeka Innocent, ya dora laifin shigarsu yajin aikin a kan jan kafar Gwamnatin Tarayya wajen biyan bukatunsu da suka jima da gabatar mata. Dokta Orji ya ce sai da kungiyar ta kara wa’adin da suka ba gwamnati da mako biyu domin ta biya bukatun nasu, amma duk da haka, sai da ta kai ga sun yi yajin aikin gargadi na kwana biyar daga ranar 17 zuwa 21 ga watan Yuli da muke ciki, kuma har yanzu gwamnatin ta ki yin abin da ya kamata. Ya kara da cewa kafin a kai ga haka, sai da aka shafe sama da mako bakwai ba tare da gwamnati ta aiwatar da yarjejeniyoyin da bangarorin suka kulla a zaman sulhun da ministan kwadago ya jagoranta ba, duk kuwa da cewa an sanya wa’adin aiwatar da su  Bukatun likitocin sun h

Kungiyar Kwadago Ta Kasa Za Ta Fara Gudanar Da Yajin Aiki

Image
Kungiyar Kwadago ta Najeriya NLC, ta baiwa gwamnatin tarayya wa’adin kwanaki bakwai da ta sauya duk wasu manufofin da ake ganin na yaki da talakawa, ciki har da karin farashin man fetur da aka yi a baya-bayan nan, ko kuma ta fuskanci yajin aikin gama gari daga ranar 2 ga watan Agusta. Kungiyar kwadago ta NLC ta umurci dukkanin kungiyoyin ta da kuma majalisun jihohi da su gaggauta fara shirin daukar ma’aikata da sauran ‘yan Najeriya da suka hada da kungiyoyin farar hula don gudanar da yajin aikin da za a dade da gudanar da zanga-zanga idan har gwamnati ta gaza biyan bukatunta. Jaridar Nigerian Tracker ta rawaito cewa wannan na daya daga cikin shawarar da aka cimma a taron kwamitin tsakiya na NLC, CWC, wanda aka gudanar a ranar Talata, 25 ga watan Yuli, a gidan ma’aikata na Abuja. Cikakken labarin zai zo muku nan gaba 

Yajin aikin likitocin Najeriya ya jefa majinyata a halin kunci

Image
Tarin asibitoci a sassan Najeriya sun fada halin garari saboda karancin likitocin da ke duba marasa lafiya sakamakon yajin aikin gargadin da kungiyar likitoci masu neman kwarewa ta NARD ke yi kasar, inda bayanai ke nuna cewa tuni majinyatan da ke bukatar kulawar gaggawa suka sauya akalar duba lafiyarsu zuwa asibitoci masu zaman kansu sakamakon cunkoson da ake gani a asibitocin gwamnati. A larabar da ta gabata ne mambobin kungiyar ta NARD suka tsunduma yajin aikin a wani yunkuri na nuna bacin ransu game da rashin cika musu alkawuran da ke tsakaninsu da gwamnati ciki har da karin albashi da akalla kasha 200. Sai kuma yunkurinsu na kalubalantar kudirin dokar da ke gaban Majalisar kasar da ke shirin kange daga fita ketare don yin aiki har sai bayan sun yi aikin shekaru 5 a cikin Najeriya. Haka zalika kungiyar likitocin na bukatar gwamnatin Najeriyar ta biya mambobinta bashin kudaden albashin da suke binta tun shekarar 2015 baya daukar tarin ma’aikatan bangaren lafiya saboda kar

Dillalan Man Fetur Sun Lashe Amansu Kan Shiga Yajin Aiki

Image
’ Yan sa’o’i bayan umartar mambobinta su rufe ilahirin gidajen man fetur a Najeriya, Kungiyar Dillalan Man Fetur ta Kasa (IPMAN) ta bukaci a bude gidajen a ci gaba da sayarwa. Aminiya ta rawaito yadda a ranar Talata kungiyar ta bukaci a rufe ilahirin gidajen man da ke kasar nan take sannan a fara yajin aiki, kamar yadda wata sanarwa da Shugaban kungiyar na kasa, Mohammed Kuluwa, ya fitar ranar Talata. IPMAN ta ce, “Sakamakon mawuyacin halin da muka tsinci kanmu a ciki wajen samo man da kuma sayar da shi da tsada, da kuma yadda hukumomi ke tilasta mana sayar da shi a kan farashin da muke faduwa. “Muna umartar ilahirin mambobinmu da su dakatar da sayar da mai, sannan su dakatar da biyan kudin duk wani man da suka riga suke kokarin sarowa daga yanzu har sai abin da hali ya yi.” To sai dai ’yan sa’o’i bayan waccan sanarwar, IPMAN ta yi mi’ara koma baya. “Bayan tattaunawa da hukumomi masu ruwa da tsaki, muna umartar gidajen mai da su bude su ci gaba da sayarwa, yayin da uwar kun

Malaman Makaranta Sun Fara Yajin Aiki A Ingila Kan Karin Albashi

Image
Malaman makaranta a Ingila da yankin Wales sun sanar da tsunduma yajin aiki daga watan Fabrairu mai zuwa saboda karin albashi. Kungiyar malaman mai suna (NEU) ta ce mambobinta sun amince da gagarumin rinjaye a fara yajin aikin har sai an yi musu karin da zai yi daidai da yanayin hauhawar farashin kayayyaki a kasar. Bayan wata 11, farashin kayayyaki ya sauka a karshen 2022 a Najeriya – NBS Kotu ta yanke wa mutum 6 hukuncin kisa ta hanyar rataya a Osun Sanarwar na zuwa ne a daidai lokacin da kungiyoyin ma’aikatan gwamnatin kasar da dama ke guna-guni kan karancin albashi. “Mun tabbatar gwamnati ta san akwai bukatar a gyara albashin malaman makaranta,” in ji Kevin Courtney, Babban Sakataren NEU, yayin wani taron kungiyar da aka watsa kai tsaye. Shugabannin kungiyar dai na shirin ganawa da Ministan Ilimin kasar ranar Laraba. Shi ma wani Sakataren kungiyar, Mary Bousted, ya ce, “Sun san ba da wasa muke ba. Da gaske muke yi wajen kokarin kare ayyukanmu.” Kungiyar dai ta sanar da f

Gwamnatin Soja ta fi ta farar hula tausayin malaman Jami'a - ASUU

Image
Shugaban Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Kasa (ASUU), Farfesa Emmanuel Osodeke, ya ce gwamnatocin mulkin soja na baya a Najeriya sun fi ta farar hula mai ci a yanzu tausayin su. Ya bayyana haka ne ranar Alhamis a Abuja, yayin kaddamar da wasu littattafan manyan makarantu guda 50 da wasu marubuta suka wallafa. Hukumar da ke Kula da Manyan Makarantu ta Najeriya (TETFund), ce dai ta dauki nauyin wallafa littatafan. A cewar Shugaban, “A shekarar 1992, lokacin da muka yi yajin aiki, sai muka bukaci a kalubalance mu, mu kawo mafita kan yadda za a samo kudaden da za a aiwatar da yarjejeniyoyin da aka amince da su. “Haka aka yi kuwa suka kalubalanci ASUU, inda ko kwana uku ba a yi ba muka kawo batun kafa TETFund, wacce kuma gwamantin mulkin soja ta wancan lokacin ta amince. Ni ina ga gwamnatin soja ta ma fi ta farar hula tausayinmu. “Yadda aka yi aka sami hukumar TETFund ke nan. An rattaba hannu a kan kudurin ya zama doka a 1993. Sai da ASUU ta sake komawa yajin aiki a karo na uku kaf