Posts

Showing posts with the label Shugaban Ma'aikatan Fadar shugaban kasa

Abdulmumin Jibrin Kofa Ya Taya Femi Gbajabiamila Murnar Sabon Mukamin Da Ya Samu

Image
A madadin abokinka, zababben dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Kiru da Bebeji ta jihar Kano, Abdulmumin Jibrin Kofa PhD (Jarman Bebeji) da iyalansa da masoyan mazabar Kiru da Bebeji sun hada kai da miliyoyin yan Najeriya domin taya ka murnar wannan nadi. A sanarwar da mai magana da yawun Zababben Dan Majalisar, Isah Sulaiman Kofa ya sanyawa hannu, ta ce Ba mu yi mamakin nadin nasa ba lalle ya sanya kwarya a gurbinta. Nasarorin da ka samu a matsayinka na dan majalisa ta 5 da 6, a matsayinka na shugaban marasa rinjaye a majalisa ta 7, a matsayinka na shugaban masu rinjaye a majalisar wakilai ta 8 da kuma matsayinka na kakakin majalisar wakilai ta tara. A tarihi, mafi kyawun kakakin Najeriya ya taba samarwa. Wannan tarihi na gogewa da sadaukarwar da ka yi cikin kyawawan shekaru ashirin da ka kasance a cikin majalisar wakilai.  Amincewarmu a gare ka ba ta kau da kai za ka kafa sabon tarihi a matsayin shugaban ma’aikatan fadar shugaban tarayyar Najeriya da ya taba samar