Posts

Showing posts with the label #hajj2023

Labari da dumiduminsa: Ranar Talata Ake Sa Ran Fara Dawo Da Alhazan Najeriya Gida

Image
Injiniya Goni shugaban kula da harkokin sufurin jiragen sama na hukumar alhazai ta kasa NAHCON ne ya sanar da hakan a taron bayan Arafah da yammacin Asabar a birnin Makkah. Ya ce, za a yi amfani da ka’idojin wanda ya zo a farko shi ne Zai koma a farko a wajen fitar da alhazai zuwa Najeriya bayan kammala aikin Hajjin. Injiniya Goni ya ci gaba da cewa, mahukuntan Saudiyya suna da manufar cewa a cikin makonni biyun farko jiragen ba za su yi aiki sosai ba saboda yawan zirga-zirgar jiragen sama da kuma yawan jiragen da suke gudanar da aikin kwashe alhazai daga nahiyoyi da kasashen duniya daban-daban. kuma kusan dukkansu suna tashi daga filin jirgin sama guda É—aya wanda shine filin jirgin sama na Sarki Abdulaziz, Jeddah. Ya ce duk da cewa an bai wa masu jigilar Alhazan Najeriya izinin jigilar maniyyata daga filin jirgin saman Madina, amma hakan ya zama doka, domin kusan kashi casa’in da takwas na alhazan Nijeriya sun riga sun ziyarci Madina, kuma a sake jigilar su zuwa Madina abi