Search This Blog

Showing posts with label Zaben 2023. Show all posts
Showing posts with label Zaben 2023. Show all posts

Saturday, 23 September 2023

Darussa Daga Siyasar Kano Ta 2023 - Dr Sa'idu Ahmad Dukawa

Tun lokacin da Injiniya Abba Kabir Yusuf ya zama gwamnan Kano daga zaben da aka gudanar a watan Maris na wannan shekarar (ta 2023) har izuwa ranar Laraba, 20/9/23, siyasar Kano (wacce ake yiwa taken “sai Kano!”) ta dada zafafa fiye da ko da yaushe a wannan zubin dimokaradiyyar (ta Jamhuriya ta hudu). A bisa fahimtata, dalilai kamar shida ne suka janyo haka. 

Za mu yi bitarsu a takaice domin amfanin gaba.

1. Zafin hamaiyar siyasa tsakanin Senator Rabiu Musa Kwankwaso da Dr. Abdullahi Umar Ganduje. Wannan ta sa wadannan jagororin na Kano guda biyu sun fifita bukatun kansu, na neman wani ya ga bayan wani a siyasance, fiye da bukatar da Kano take da ita na su hada kansu domin su samarwa da Kano zaman lafiya da cigaba mai dorewa. 

A dalilin haka magoya bayansu sun dukufa wajen ganin jagoransu ne a sama ta kowane hali. Don haka cece-kuce ya kazanta a tsakanin juna. Da Allah zai sa idan aka kai karshen tirka-tirkar wadannan manyan biyu su yafewa juna su yi sulhu a tsakaninsu da zai fi kyau ga Kano da ma Kasa baki daya.

2. Karancin tazara tsakanin APC da NNPP ya sa kowa yana ganin ba zai ja da baya ga dayan ba. Wannan ce ta sa APC ba ta dangana ba game da zaben 2023 ta garzaya kotu. Sabanin abinda ya faru a zaben 2003, lokacin da Malam Ibrahim Shekarau ya karba daga hannun Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso, wanda tazara tsakanin ANPP da PDP ta sa PDP ta saduda ba tare da ta je kotu ba. Haka ma a 2011, lokacin da Kwankwaso ya dawo ya karba daga hannun Shekarau. Ko da yake ANPP ta garzaya Kotu, amman shari’ar ba ta dauki hankali kamar a wannan karon ba, saboda sauran abubuwan da suka faru a wannan karon ba su faru a wancan lokacin ba. 

To amman fa karancin tazara a tsakanin jam’iyyu biyu bai kamata ya zama matsala ba. Hasali ma kamata ya yi ace ya zamo riba saboda jam’iyya mai mulki ta rika yin taka-tsantsan, sannan hamayyar siyasa ta sa a inganta shugabanci. Kuma idan an samu sauyi a zabe a dada samun ingancin shugabanci. Amman fa duk sai hamayyar da ake yi akan manufa ake yinta ta neman cigaban kasa da al’umma baki daya.

3. Yadda gwamnatin NNPP ta dauki wasu matakai a cikin garaje ya haifar da ta’azzara a hamayyar da ake yi a siyasar Kano. Alal misali, yadda aka kaddamar da bincike akan tsohon gwamna Ganduje nan take zai bashi hoton kamar ana son a ga bayansa ne a siyasance, don haka dole zai dauki matakai ba kawai na kare kansa ba amman har na ganin ya ga bayan abokan hamayyarsa a siyasance. Ya kamata ace an gane cewar idan Kwankwaso yana da gwamnatin Kano, Ganduje kuma yana tare da gwamnatin Tarayya. Da ace hada kansu suka yi wajen nemarwa Kano abinda zai amfaneta da ya fi su tsaya gwada kwanji. Akwai fatan bayan wannan dambarwas a samu daidaito a tsakanin shumagabannin biyu. Wani misalin shine yadda aka yi garaje wajen yin rusau daga hawan gwamnatin.
 Anan ba rusau dinne a karan kasa matsala ba. Amman rashin tsayawa a tantance, a kare wadanda ba su da hakki daga fadawa cikin hasarar da ba suji ba, ba su gani ba. Akwai fatan duk wani aiki da za a yi anan gaba a yi la’akari da kaucewa daukar hakki. Zai rage cece-kuce da fadawa cikin matsalar da za a iya kauce mata.

4. Karyewar kawancen siyasa tsakanin Shugaban Kasa, Bola Ahmad Tinubu, da Senator Rabiu Musa Kwankwaso ba za ta rasa nasaba da dagulewar harkokin siyasa a Kano ba. Da ace an yi wannan kawancen da hamayya za ta ragu tsakanin jagororin biyu, ko da ba ta kare gaba daya ba. Amman wannan karayar ta haifar da Karin masu hamayya da Senator Kwankwaso. 

Don haka siyasar ta Kano ta dada zafafa. Anan ‘yan Majalisar Tarayya na jam’iyyar NNPP suna da rawar da za su taka wajen samar da sasanci tsakanin Madugunsu da Shugaban Kasa. Yana da kyau su yi kokarin yin hakan. Su sun san hanyoyin da ake bi wajen yin hakan. Bukatar da Kano take da ita na neman zaman lafiya da karuwar arziki ita ya kamata a fifita.

5. Yakin ‘yan Media (Sojojin Baka) na bangarorin biyu ya ta’azzara hamayya a siyasar Kano. Yadda kowane bangare ya rika shiga kafafen yada labarai yana yanke hukunci akan shari’ar da ake yi ta zabe bai dace ba ko kadan. Yana da kyau a samu wasu su nemi Kotu ta haramta irin wannan dabi’ar a Shari’un da za a yi a nan gaba.

6. Kalaman tinziri da wasu jami’an gwamnati suka yi a gabanin yanke hukuncin shari’ar zaben na gwamnan Kano matsalace babba. Barazana ce ga tsarin shari’a da ma shugabanci baki daya. Wadanda suka yi wannan kalaman ba su yi la’akari da cewar gwamnatin jiha suke wakilta ba, kuma gwamnatin Taryya suke nunawa yatsa! Da sun yi la’akari da abinda yake samun ‘yan kungiyar IPOB, na yankin Igbo, da watakil ba su yi barazanar ba. Anan dole ne a yabawa gwamna Abba Kabir Yusuf game da matakin ladabtarwa da ya dauka nan take. Akwai bukatar duk mai kaunarsa ya kiyayi irin wannan kalaman daga nan har a gama appeal, da ma bayan an gama.

A karshe akwai bukatar ‘Yansiyasa su karanta dokar zabe ta Kasa, da ma sauran dokokin da suke da alaka da zabe, su yi kokari su fahimce su, su bisu sau da kafa. Wannan zai rage matsalolin zabe wadanda suke haifar da sai an kai ga shari’ar zabe. Haka kuma zai sa a fi fahimtar hukuncin da Kotunan zabe suke yankewa.

Muna fatan Allah Ta’ala ya tabbatar da zaman lafiya da karuwar arziki a Kano da Kasa baki daya.

Saturday, 15 April 2023

Alhassan Doguwa ya yi tazarce a karo na hudu

 


Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Tarayya Alhassan Ado Doguwa ya ci zabe a karo na biyar.

Baturen zaben da aka kammala a ranar Asabar, Farfesa Sani Ibrahim, ya ce Alhassan Ado Doguwa ya yi nasarar komawa kan kujerarsa ne bayan ya samu kuri'u 41,573 a yayin da dan takarar jam'iyyar NNPP, Yusha'u Salisu, ya zo na biyu da kuri'u 34,831.


Idan za a iya tunawa bayan zaben da aka gudanar ranar 25 ga watan Maris, INEC ta bayyana Doguwa a matsayin wanda ya yi nasara.


Amma daga bisani aka janye nasarar Doguwa bayan da baturen zaben, Farfesa Ibrahim Yakasai ya cewa tursasa masa bayyana sakamakon aka yi, don haka bai samu nutsuwar yin lissafin kuri'un da aka jefa yadda ya kamata ba, kasancewar rayuwarsa da ta ma'aikata na cikin hadari a lokacin.


Amma daga baya da aka yi lissafi aka gano zaben bai kammalu ba saboda kuri'un da aka soke sun zarce tazarar da ke tsakanin kuri'un Doguwar da na Yusha'u.


Hakan ne ya sa aka kammala zaben a yau, wanda Alhassan Ado Doguwa ya yi nasara.

Tuesday, 28 March 2023

Zababben Gwamnan Jihar Kano Abba Kabir Yusuf na ya al'ummar Kano domin su Karbar Shaidar Cin Zabensa

Zababben Gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf, wanda aka fi sani da Abba Gida Gida yana gayyatar dumbin magoya bayansa, mambobin jam'iyyar NNPP da kuma manyan masu ruwa da tsaki, zuwa gabatar da takardar shaidar cin zabe ga dukkan 'yan takarar da suka ci zabe a ranar Asabar 18 ga wata.

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) a Kano ta shirya ranar Laraba 29 ga Maris, 2023 da karfe 10 na safe a sakatariyar INEC don bayar da shaidar cin zabe ga zababben gwamna da mataimakinsa da ‘yan majalisar jiha.

Kakakin zababben gwamnan jihar Kano, Sanusi Bature Dawakin-Tofa, a wata sanarwa a ranar Talata ya ce za a gudanar da taron ne a dakin taro na INEC da karfe 10:00 na safe.

Ya kuma bukaci magoya bayan jam’iyyar NNPP da duk wadanda aka gayyata, wadanda suka shahara da son zaman lafiya da bin doka da oda, da su rika gudanar da harkokinsu cikin tsari a lokacin bikin da kuma bayan bikin, tare da yi wa kowa fatan alheri.

SABATURE

Tuesday, 14 March 2023

Sufeto Janar Ya Sake Turo Usaini Gumel A Matsayin Sabon Kwamishinan 'Yan Sanda Na Kano


Sufeto Janar na ‘yan sanda, Usman Alkali, ya sake soke turo kwamishinan ‘yan sandan Kano.

A wata sanarwa da aka fitar a ranar Litinin, Sufeto Janar din ya soke aika Feleye Olaleye a matsayin kwamishinan ‘yan sandan Kano tare da sanya CP Ahmed Kontagora a matsayin wanda zai maye gurbinsa.

Sai dai a wata siginar da aka sake fitarwa a daren jiya, sufeto janar din ya nada CP Usaini Gumel a matsayin wanda zai jagoranci rundunar 'yan sanda ta Kano lokacin zabukan gwamnoni da na ‘yan majalisar jiha a jihar.

A ranar 8 ga Maris, bayan zanga-zangar da ‘yan adawa suka yi, IGP ya sauya matakin da aka tura CP Balarabe Sule, tsohon babban jami’in tsaro ga gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje, a matsayin wanda zai maye gurbin CP Mohammed Yakubu

A cikin sabuwar takardar da aka fitar mai dauke lamba TH.5361/FS/FHQ/AB3/SUB.6/146, Mista Alkali kuma ya sake yin wasu ƙananan canje-canje a cikin umarnin.

IGP ya umurci DCP Auwal Musa da ya karbi DCP Nuhu Darma a matsayin mataimakan kwamishinan ‘yan sanda mai kula da ayyuka da binciken manyan laifuka (CID)

Daily Nigerian 

Thursday, 9 March 2023

2023: Idan Na Zama Gwamna Zan Bawa Kananan Hukumomin 'Yancinsu - Gawuna

Mataimakin gwamnan jihar Kano kuma dan takarar gwamna na jam’iyyar  APC, Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya yi alkawarin baiwa kananan hukumomin jihar ‘yancin cin gashin kansu idan aka zabe shi a matsayin gwamna.

Ya bayyana hakan ne a lokacin da yake gabatar da shirin gidan talabijin na NTA cikin shirin "The Balot".

"Ƙananan Hukumomin wani bangare ne na gwamnati kuma su ne matakin kusa da jama'a wanda ke taimakawa hatta ci gaba da rarraba albarkatu da ayyuka".

"A matsayina na tsohon shugaban karamar hukumar na san abin da ya shafi gudanar da mulkinta".

Lokacin da nake shugaban karamar hukuma, an ba ni cikakkiyar dama nayi  aiki. Hakan ya sa muka samu nasarori da dama don haka idan aka zabe mu a matsayin Gwamna zan mayar da martani kamar yadda Gawuna ya bayyana”.

A sanarwar da babban sakataren yada labaransa, Hassan Musa Fagge ya fitar, Gawuna Ya kara da cewa shi ne wanda ya fi cancanta kuma a shirye ya ke ya zama Gwamnan Jihar Kano bayan ya yi aiki da gwamnatocin da suka gabata kuma ya samu kwarewa da dama, duk da haka ya ba da tabbacin karfafa nasarorin da suka samu a wani bangare na manufofin ci gaba.

Gawuna ya kuma bukaci masu kada kuri’a da su guji tashin hankali su gudanar da rayuwarsu cikin kwanciyar hankali da lumana a lokacin zaben.


Thursday, 2 March 2023

Zamu Kalubalanci Zaben Shugaban Kasa - Atiku Abubakar

Ɗan takarar shugaban ƙasa na babbar jam’iyyar hamayya a Najeriya, PDP, Atiku Abubakar ya ce dole ne kowa ya ƙalubalanci zaɓen da aka yi na ranar 25 ga watan Fabarairu.

A taron manema labarai da ya gabatar a Abuja, tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya ce, abin da ya faru a kan zaɓen fyaɗe ne aka yi wa dumukuradiyya.

Atiku ya ce, a tarihin ƙasar wannan shi ne zaɓe mafi muni da aka taɓa yi, wanda kuma dama ce ta sake daidaita Najeriya.

Amma kuma hukumar zaɓen ƙasar, INEC ta lalata tare da watsa wannan dama da buri na ‘yan Najeriya.

Ɗan takarar na PDP, ya ce zaɓen ya kasa kaiwa matsayi da matakin da aka sa rai zai kai.

Sannan ya ce lauyoyinsu suna duba lamarin kafin su san matakin da za su ɗauka na gaba.

Ya ce idan har ya je kotu ba a yi masa adalci ba to zai bar su da Allah.

Za mu kawo muku karin bayani a nan gaba.
BBC 

Wednesday, 1 March 2023

Kotun Magistare A Kano Ta Aike Da Alasan Ado Doguwa zuwa Gidan Kaso

Kotun Magistare dake Kano, ta aike da shugaban masu rinjaye na majalisar Wakilai, Alasan Ado Doguwa zuwa gidan kaso kafin ta bayar da belinsa. 

SOLACEBASE reports that the defendant, Alhassan Doguwa is standing trial on several offences that include, criminal conspiracy, culpable homicide, unlawful possession of fire arm, mischief and public disturbance

Babban Alkalin Kotun, Ibrahim Mansur Yola, shi ne ya aike da wanda ake zargin har zuwa ranar 7 ga watan Mayu, lokacin da za a saurari batun Karbar belinsa 


Zabe - Gawuna Ya Taya Zababben Shugaban Kasa Tinubu Murna


Mataimakin gwamnan jihar Kano kuma dan takarar gwamna na jam’iyyar APC Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya taya zababben shugaban kasa Sen.Bola Ahmed Tinubu da mataimakin zababben shugaban kasa Sen.Kashim Shettima murnar nasarar da suka samu a zaben shugaban kasa da aka gudanar a ranar Asabar. 25 ga Fabrairu, 2023.

 

"Ni da kaina da abokina Hon.Murtala Sule Garo ina muku fatan nasara yayin da kuke daukar nauyin sabunta fata tare da addu'ar Allah Madaukakin Sarki Ya kara muku hikima, karfi, jagora da jagora don aiwatar da aikin da aka dora muku".

 

"Jagaban, kai ne mutumin da ya dace a halin yanzu, nasararka nasara ce ga dimokuradiyya, ka yi aiki tukuru domin samun nasarar jam'iyyarmu ta APC."

 

"Ka tabbatar da cewa kai dan dimokradiyya ne na gaske wanda ya nuna jajircewa, kishi da sadaukarwa ga hidima da ci gaban kasarmu."

 

"Mun gode muku bisa jajircewarku da tsayin dakanku domin mun yi imanin cewa kuna da kyakkyawar niyya don cika alkawuran da kuka yi a lokacin yakin neman zabe".

 

Gawuna ya kuma mika godiyar sa ga al'ummar jihar Kano dangane da zaben jam'iyyar APC a zaben da ya gabata.

 

"Kun yi shi a baya kuma mun yi imanin za ku sake yin hakan don haka muna gode muku da ci gaba da ba ku goyon baya da hadin kai, tare za mu kai ga wani matsayi mai girma Gawuna."

 

CPS

Tuesday, 28 February 2023

Nasarar Tinubu Ta Yi Nuni Da Yadda Dimokwaradiyya Ta Yi Aikinta - Ganduje

Gwamna Ganduje ya bayyana Nasarar dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a zaben 2023, a matsayin shugaban kasa a Najeriya, ta nuna yadda aka yi dimokaradiyya ta gaskiya. 

A wani martani ga nasarar da Tinubu ya samu, Gwamna Ganduje ya yaba da gwagwarmayar siyasa da jajircewar daular siyasar Tinubu, wadda ta samar da wasu abubuwa daga ko’ina a fadin kasar nan, wajen tabbatar da cewa dan takarar shugaban kasa ya yi nasara baki daya.

“Sahihancin jarin Asiwaju Bola Ahmed Tinubu a kan ɗan adam, ci gaban ƙasa da haɗin kan ƙasa ya taka muhimmiyar rawa wajen fifita shi ga dukkan sassan ƙasar,” in ji shi.

Ya kara da cewa, “Yakin da Tinubu ya kwashe shekaru da dama yana yi na maido da mulkin dimokuradiyya a kasar nan, ‘yan Najeriya sun fahimta sosai. Don haka, muna ganin hikima da kuma dalili mai kyau na jinginar da makomarmu gare shi.”

Yayin da yake tabbatar da cewa, zababben shugaban kasar zai bullo da dabarun tunkarar matsalolin da suka addabi al’ummar kasar nan, Gwamna Ganduje ya yabawa shugabannin jam’iyyar da mambobin jam’iyyar da suka tsaya tsayin daka har zuwa wannan lokaci.

Tinubu, a cewar Ganduje, “Mai ƙwazo ne mai dabara, maginin mutum da sararin samaniya, ƙwararren shugaba na siyasa, shugaba mai yada al’umma, mai jurewa da tabbatar da dimokuradiyya mai dorewa da ci gaba kuma ƙwararren mai motsawa.”

Da wadannan abubuwan da suka gabata da ma wasu da dama da suka yi tasiri wajen ganin wanda ya lashe zaben shugaban kasa, Gwamna Ganduje ya kara bayyana cewa, “Tare da zababben shugaban kasarmu, Tinubu, ya jagoranci dimokuradiyya mafi girma a Afirka, tabbas nahiyarmu za ta ci gajiyar dimbin kwarewa. domin ci gaban nahiyar.

"Nasarar da Tinubu ya samu ba wai kawai kasarmu ta uwa ta Najeriya za ta amfana ba, zai kuma zama wani kwarin gwiwa ga Afirka, a matsayinta na nahiya da kuma aiwatar da tsarin dimokuradiyya a duniya," in ji shi.

Hukumar DSS Ta Kama Alasan Ado Doguwa

Hukumar tsaro ta farin kaya (DSS) ta kama shugaban masu rinjaye na majalisar wakilai Alhassan Dogowa, saboda zargin kisan wasu magoya bayan jam’iyyar adawa a yankin.

 Majiyarmu ta rawaito cewa an kama Doguwa ne a filin jirgin sama na Malam Aminu Kano , a kan hanyarsa ta zuwa kasar Saudiyya domin gudanar da aikin umarah a ranar talata.

 Kamen ba zai rasa nasaba da kisan da aka yi wa magoya bayan ‘yan adawa kusan 15 a karamar hukumar Tudunwada a lokacin zaben da aka kammala ba .

 Rahotanni sun ce an kulle wasu daga cikin mutane a wani gini inda aka kona su kurmus, lamarin da ya sa aka gagara kubutar
Kadaura24 

Wednesday, 25 January 2023

Take-Taken Da Ake Nufi Da Karancin Mai Da Sauya Fasalin Naira —Tinub

Dan takarar Shugaban Kasa karkashin Jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, ya yi zargin matsalar karancin mai da ake fuskanta da sauya fasalin wasu takardun Naira da aka yi, take-taken neman wargaza Zaben 2023 ne kawai.

Tinubu ya bayyana haka ne yayin gangamin yakin neman zaben APC da ya gudana ranar Laraba a Abeokuta, babban birnin Jihar Ogun.

Na tafka kuskure a tafiyar Buhari, ba zan maimaita da Tinubu ba — Naja’atu
Muna da hujjoji kan cewa Tinubu tsohon mai laifi ne – Dino Melaye 
“Ba sa son zaben ya gudana. So suke su wargaza shi. Za ku bari hakan ta faru?, in ji Tinubu.

Dan takarar ya ce yana da yakinin matsalar karancin fetur ba za ta hana ’yan Najeriya zuwa kada kuri’a ba ranar zabe.


“Sun fara bullo da batun ‘babu mai, kar ku damu, idan babu mai za mu taka da kafa zuwa wajen zabe.

“Idan kun ga dama ku kara kudin mai, ko boye man ko kuma ku canza wa naira launi, za mu ci zabe,” in ji shi.

Wednesday, 18 January 2023

Idan Mijina ya Gza bayan Shekara hudu, Ka da ku Sake Zabarsa - Matar Tinubu

 


Mai dakin dan takarar Shugaban Kasa na jamiyyar APC, Sanata Oluremi Tinubu, ta shawarci yan Najeriya da kada su sake zaben mijinta a karo na biyu idan ya gaza tabuka komai bayan shekara hudu.

Oluremi ta yi wannan kira ne a wajen gangamin yakin neman zaben Tinubu/Shettima na matan shiyyar Kudu maso Gabas wanda ya gudana a Owerri, babban birnin Jihar Imo.

Ta ce, “A ajiye batun addini a gefe, ni Kirista ce. Ko kun taba tunanin cewa wata rana za a samu ‘yan takara Kirista da Kirista?

“Me ya kamata ya zama madogara? Tun da mun jarraba ‘yan takara Musulmi da Kirista, bari mu jarraba wannan ma mu gani sannan bayan shekara hudu idan ba su tabuka komai ba kuna iya yin waje da su,” in ji ta.

Saboda a cewarta, “Idan ana da mutum mai tsoron Allah, ba wai Kirista ko Musulmi ba, amma dai mutum mai tsoron Allah. Idan mai tsoron Allah ya kasance rike da mulki zai ba ku kulawar da ta dace.

A matsayinta na wadda ta yi wa Najeriya hidima a matsayin matar Gwamna da kuma Sanata, Oluremi ta bai wa matan Najeriya tabbacin za su samu kaso mai tsoka muddin Tinubu/shettima suka kafa gwamnati.

“Yanzu lokacin yi wa Najeriya aiki ne. Ba wasa muke ba. Za mu tuna da mata kuma ina ba ku tabbacin cewa Asiwaju zai tuna da ku.

“Tinubu/Shettima na da kyakkyawan tanadi ga matasa. Za mu yi aiki da kowace shiyya a kan bukatunta,” in ji Oluremi.

Da yake tofa albarkacin bakinsa a wajen taron, Gwamnan Jihar Imo, Hope Uzodimma, ya yi kira ga matan shiyyar Kudu maso Gabas da su yi farar dabara sannan su zabi dan takarar shugabancin kasa na APC a zabe mai zuwa.

Monday, 9 January 2023

Kuyi amfani da kalaman da al'uma zasu gamu dasu wajan yakin neman zabe: Mai Martaba Sarkin Kano.

Mai martaba sarkin kano Alhaji Aminu Ad Bayero ya yi kira ga masu neman kujerun mulkin kasar nan da su tabbatar sunyi kalamai da al'umma za su gamsu da su wajen neman kuri'ar alumma a zaben shekarar 2023.

A sanarwar da Sakataren yada labaran Masarautar Abubakar Balarabe Kofar Naisa ya sanyawa hannu, ta ce Sarkin ya bayyana haka ne lokaci da dan takarar shugaban kasa na jam'iyar SDP Adewale Adebayo da dantakar kujerar gwamnan jihar Kano Dr. Muhammad Bala gwagwarwa yayin da su ka  ziyar ce shi a fadar sa.

Alhaji Aminu Bayero, ya kuma nemi da duk wani dake neman kujerar da yasan cewa Allah ne ke bayar da Mulki bawai karfin ikon tada zaune tsayeba.

Da yake nasa jawabin, dan takarar Gwamna na jam'iyyar ta SDP Bala Muhammad Gwagwarwa ya ce sun ziyarci fadar sarkin ne domin neman tabaraki da addu'ar.

A wani cigaban kuma Martaba Sarkin kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya nada Dr. Malam Umar Ibrahim Indabawa  a matsayin sabon limamin  Masallacin Darul hadis dake Unguwar Tudun Yola a Karamar  Hukumar Gwale.


Sunday, 1 January 2023

2023: Amurka Za Ta Mara Wa Najeriya Baya A Harkar Zabe



Gwamnatin Kasar Amurka ta ce za ta mara wa Najeriya baya dangane da zaben 2023 don tabbatar da masu kada kuri’a sun samu aminci a yayin zaben.

Amurka ta bayyana hakan ne ta bakin ofishin jakadancinta a Najeriya.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN), ya rawaito Amurka za ta mara wa kasar baya ne karkashin shirin ‘Vote023’.

Vote023 shiri ne na musamman don wayar da kan jama’a kan harkokin zabe musamman ganin yadda zaben 2023 ya karato.

Ochu-Baiye ta ce abin a yaba ne ganin Ofishin Jakadancin Amurka ya amice su yi aiki tare don wayar da kan ’yan kasa kan zaben 2023.


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...