Posts

Showing posts with the label Yakin Sudan

Yakin Sudan: Sojoji Da ’Yan Tawaye Za Su Koma Teburin Sulhu A Saudiyya

Image
Sojoji da mayakan RSF da ke yakar juna a Sudan za su koma kan teburin sulhu ranar Lahadi bayan sun kwana suna ba-ta-kashi a Khartoum, babban birnin kasar. Wani babban jami’in gwamnatin Sudan ya ce za su koma tattaunawar ne bayan barkewar yaki tsakaninsu duk da yarjejeniyar da suka sanya hannu na kare fararen hula da ayyukan jin kai. Jami’in ya bayyana cewa kasar Saudiyya mai masaukin baki ta gayyaci Babban Hafsan Sojin Sudan, Janar Abdel Fattah al-Burhan zuwa babban taron kasashen Larabawa da zai gudana a birnin Jidda ranar Juma’a. Sai dai wasu jakadun kasashen Larabawa sun bayyana cewa ba a tsammanin zuwan Janar Burhan zai halarci taron ba saboda dalilan tsaro. An gayyaci Janar Burhan ne a matsayinsa na shugaban kwamitin rikon kasar, wanda aka dora wa alhakin tsara yadda za a mika mulki ga zababbiyar gwamnati anan gaba, Abokin hamayyarsa kuma shugaban mayakan RSFk, Janar Mohamed Hamdan Dagalo kuma shi ne mataimakinsa a kwamitin. Wani jakadan kasar Saudiyya ya bayyana cewa kawo yanzu d

Yakin Sudan: Akwai Yiwuwar Maniyyata Su Kara Biyan Wasu Kudin

Image
  Hukumar Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta tabbatar da cewa yaƙin da ake yi a kasar Sudan zai shafi jigilar maniyyatan Najeriya na bana, wanda ka iya sanadin karin kudin kujerar. A ranar Talata hukumar da kamfanonin sufurin jiragen sama na cikin gida suka rattaba hannu a kan yarjejeniyar jigilar mahajjatan ta bana A makon jiya dai sun gaza yin hakan saboda batun ƙarin kuɗi. Sai dai hukumar ba ta bayyana ko matakin na nufin, maniyyata aikin hajji ne za su biya ƙarin kuɗin da dogon zagayen zuwa kasa mai tsarki ko a’a ba. Kwamishinan Tsare-tsare da Gudanar da Gikin Hajji a hukumar, Abdullahi Magaji Hardawa, ya ce har zuwa yanzu ba a cimma matsaya kan ko mahajjata ne za su yi ƙarin kuɗin ba. A cewarsa, matuƙar ba a buɗe sararin samaniyar kasar Sudan ba, har aka fara jigilar maniyyatan bana daga Najeriya, to dole sai jiragen sama sun yi zagaye, wanda zai haddasa ƙarin kuɗi. Jami’in ya ce babban hatsari ne jirgin sama ya ratsa ta sararin samaniyar Sudan, shi ya sa hukumomin ƙasar suka dakatar