Search This Blog

Showing posts with label Yakin Sudan. Show all posts
Showing posts with label Yakin Sudan. Show all posts

Saturday, 13 May 2023

Yakin Sudan: Sojoji Da ’Yan Tawaye Za Su Koma Teburin Sulhu A Saudiyya


Sojoji da mayakan RSF da ke yakar juna a Sudan za su koma kan teburin sulhu ranar Lahadi bayan sun kwana suna ba-ta-kashi a Khartoum, babban birnin kasar.

Wani babban jami’in gwamnatin Sudan ya ce za su koma tattaunawar ne bayan barkewar yaki tsakaninsu duk da yarjejeniyar da suka sanya hannu na kare fararen hula da ayyukan jin kai.

Jami’in ya bayyana cewa kasar Saudiyya mai masaukin baki ta gayyaci Babban Hafsan Sojin Sudan, Janar Abdel Fattah al-Burhan zuwa babban taron kasashen Larabawa da zai gudana a birnin Jidda ranar Juma’a.

Sai dai wasu jakadun kasashen Larabawa sun bayyana cewa ba a tsammanin zuwan Janar Burhan zai halarci taron ba saboda dalilan tsaro.

An gayyaci Janar Burhan ne a matsayinsa na shugaban kwamitin rikon kasar, wanda aka dora wa alhakin tsara yadda za a mika mulki ga zababbiyar gwamnati anan gaba,

Abokin hamayyarsa kuma shugaban mayakan RSFk, Janar Mohamed Hamdan Dagalo kuma shi ne mataimakinsa a kwamitin.

Wani jakadan kasar Saudiyya ya bayyana cewa kawo yanzu dai ba a fitar da sunayen wadanda za su wakilci bangarorin a zaman ba.

Rikicin da ya barke bagatatan a watan Afrilu a Sudan ya yi ajalin kusan mutum 800, tare da tilasta wasu sama da 200,000 gudun hijira zuwa kasashe makwabta.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce bayan haka wasu sama da 700,000 sun yi  gudun hijira zuwa wasu sassan kasar.

A ranar Alhamis Saudiyya da Amurka suka jagoranci sanya hannu kan yarjejeniyar tsagaita wuta tsakanin bangarorin da nufin kare fararen hula da bayar da damar ci gaba da ayyukan jin kai.

Sai dai kuma bangarorin sun ci gaba da luguden wuta a sassan birnin Khartoum, cibiyar rikicin, kafin wayewar garin Asabar.

Ana dai sa rai cewa a zaman ranar Lahadi bangarorin za su tatttauna matakan aiwatar da yarjejeniyarsu ta ranar Alhamis kan yadda za a kare fararen hula da ma’aikatan agaji da kuma janye sojoji daga yankunan fararen hula.

Za kuma a tattauna yadda za a kawo karshen rikicin, wanda zai kai ga kafa sabuwar gwamnatin farar hula a Sudan.

Bisa abin da aka saba gani, babu wani daga cikin bangarorin da ke nuna alamar sassauci, inda suke ta gwabza fada, duk da cewa sun yi yarjejeniyar tsagaita wuta.

Sai dai kawo yaznu, RSF ta yi alkawarin mutunta yarjeniyar ranar Alhamis, amma har yanzu bagaren sojojin kasar bai ce uffan ba.

AMINIYA

Wednesday, 10 May 2023

Yakin Sudan: Akwai Yiwuwar Maniyyata Su Kara Biyan Wasu Kudin


 Hukumar Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta tabbatar da cewa yaƙin da ake yi a kasar Sudan zai shafi jigilar maniyyatan Najeriya na bana, wanda ka iya sanadin karin kudin kujerar.

A ranar Talata hukumar da kamfanonin sufurin jiragen sama na cikin gida suka rattaba hannu a kan yarjejeniyar jigilar mahajjatan ta bana

A makon jiya dai sun gaza yin hakan saboda batun ƙarin kuɗi.

Sai dai hukumar ba ta bayyana ko matakin na nufin, maniyyata aikin hajji ne za su biya ƙarin kuɗin da dogon zagayen zuwa kasa mai tsarki ko a’a ba.

Kwamishinan Tsare-tsare da Gudanar da Gikin Hajji a hukumar, Abdullahi Magaji Hardawa, ya ce har zuwa yanzu ba a cimma matsaya kan ko mahajjata ne za su yi ƙarin kuɗin ba.

A cewarsa, matuƙar ba a buɗe sararin samaniyar kasar Sudan ba, har aka fara jigilar maniyyatan bana daga Najeriya, to dole sai jiragen sama sun yi zagaye, wanda zai haddasa ƙarin kuɗi.

Jami’in ya ce babban hatsari ne jirgin sama ya ratsa ta sararin samaniyar Sudan, shi ya sa hukumomin ƙasar suka dakatar da zirga-zirgar jiragen sama a kasar.

Harɗawa ya ce matuƙar aka fara jigilar maniyyata aikin hajji na bana, ba tare da an bi ta Sudan ba, za a fuskanci matsaloli guda biyu ko fiye.

“Na farko, in ba za a shiga ta sararin samaniyar Sudan ba, dole za a shiga ta wasu ƙasashe. To ƙasashen nan akasari, za a biya su kuɗin ratsawa ta sararin samaniyarsu.

“To maimakon kuɗin da za a biya na ƙasa ɗaya, wato Sudan. (A yanzu) mai yiwuwa a biya na ƙasashe da yawa. Kun ga an samu ƙarin kuɗaɗe ke nan,” in ji shi.

Na biyu, a cewarsa, tun da akwai ƙarin tazara kamar na sa’a biyu a tafiyar jirgin sama, man da jirgin yake sha ma zai ƙaru, wanda ke nufin ƙarin kuɗin jigilar alhazai.

Abdullahi Harɗawa ya ce kamfanonin jiragen sama sun sa hannu a kan yarjejeniyar jigilar aikin hajjin na bana ne bayan an daddale tsakaninsu da Hukumar NAHCON a kan matsalolin da za a iya fuskanta.

Ya ce: “Sun amince sun sa hannu ɗin, amma an yarda akwai bukatar a san yadda za a yi, a ƙara musu farashi.”

Jami’in ya ce kasanceaw maniyyata sun riga sun biya kuɗi, “bisa yadda aka tallatar masa,”  yanzu ba zai iya tabbatar da ko za a bukaci maniyyaci ya kara biyan wasu kudin ba.

“Amma dai abin da nake tabbatar muku so hi ne, akwai bukatar ƙarin kuɗi. Akwai tazara da yawa. Akwai ɗawainiya da yawa. Karin kuɗin nan daga ina zai fito? Shi ne ba a cimma matsaya ba”.

Kamfanonin sufurin jiragen saman da suka sa hannu kan yarjejeniyar sun haɗar da – Air Peace da Azman Air Services da Aero Contractor da kuma Max Air.

AMINIYA

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...