Search This Blog

Showing posts with label Mauritaniya. Show all posts
Showing posts with label Mauritaniya. Show all posts

Monday, 16 January 2023

Buhari Zai Karbo Kyautar wanzar da zaman lafiya a Mauritaniya

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari a ranar Talata mai zuwa zai karbi kyautar “Karfafa zaman lafiya ta Afirka” a birnin Nouakchott na kasar Mauritaniya.

Kakakin Shugaban, Femi Adesina ne ya bayyana hakan a cikin wata sanarwa ranar Lahadi, inda ya ce Buharin zai karbi kyautar ce saboda irin rawar da yake takawa wajen wanzar da zaman lafiya da kuma yin sulhu a kasashe daban-daban na nahiyar Afirka.

Noman masara zai yi wahala a damina mai zuwa — Kamilu Sigau
Ko sanyi na da alaka da yawaitar tashin aljanu da iskokai?
Kwamitin Zaman Lafiya na Abu Dhabi, ne dai zai gabatar wa Buhari kyautar.

An kafa kwamitin na Shugabannin Kasashe ne a shakara ta 2014 domin a lalubo hanyoyin bunkasa zaman lafiya da kwanciyar hankali a duk fadin duniya.


Adesina ya kuma ce gabanin Buharin ya karbi kyautar, Shugaban zai halarci taron kasashen Afirka kan samar da zaman lafiya, inda zai ma gabatar da makala a wajen taron.

Kakakin ya kuma ce Buhari zai bar Najeriya ne ranar Litinin, sannan ana sa ran dawowarsa ranar Laraba.

Sanarwar ta kuma ce yayin ziyarar, Buhari zai sami rakiyar ministan Harkokin Waje, Geoffrey Onyeama, da na Tsaro, Manjo-Janar Bashir Salihi Magashi (mai ritaya) da mai ba shi shawara an harkokin tsaro, Mohammed Babagana Mongunoda kuma Shugaban Hukumar Leken Asiri ta Najeriy, Ahmed Rufai Abubakar.
(AMINIYA) 


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Head of Service Urges Civil Servants to Uphold Ethical Conduct

The Head of Service, Kano State, has called on civil servants to strictly adhere to the Civil Service ethical code and show grea...