Posts

Showing posts with the label Cibiyar Bayar Da Horo Kan Ayyukan Hajji

Hukumar NAHCON Ta Bude Cibiyar Bayar Da Horo Kan Ayyukan Hajji

Image
Hukumar alhazai ta kasa NAHCON ta kaddamar da cibiyar bayar horo kan ayyukan Hajji da alhazai Cibiyar za ta horas da duk ma’aikatan da ke aikin Hajji da Umrah ta Najeriya tare da ba su takardar shaida. Haka kuma za ta samar da hanyoyin koyon sana'o'i, bunkasa sana'o'in Matasa da kuma zama wurin tuntuba a duk duniya wajen horar da aikin Hajji da Umrah. An kuma gabatar da kason farko na daliban cibiyar. Daliban sun hada da Shugaban Hukumar, da daukacin kwamishinonin zartaswa na Hukumar, mambobin hukumar da zababbun Sakatarorin gudanarwa na hukumar jin dadin Alhazai na Jahohi.  Manyan baki da dama ne suka halarci bikin, ciki har da Ministan babban birnin tarayya Abuja, Malam Muhammad Musa Bello CON; Sakataren Gwamnatin Tarayya, Boss Mustapha CFR; Jakadan Saudiyya a Najeriya,  Faisal Ibn Ibrahim Al-Ghamdy; Shugaban NAHCON, Alh. Zikrullah Kunle Hassan da Babban Sakataren Hukumar NBTE, Farfesa Idris Bugaje. (Nura Hassan Yakasai)