Search This Blog

Showing posts with label Abuja. Show all posts
Showing posts with label Abuja. Show all posts

Thursday, 18 January 2024

Kotu Ta Ba Emefiele Izinin Fita Daga Abuja

 Kotu ta sahale wa tsohonn Gwamnan CBN, Godwin Emefiele, fita daga yankin Babban Birrnin Tarayya.



Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta ba wa tsohonn Gwamnan Baban Bankin Najeriya (CBN) Godwin Emefiele, izinin fita daga yankin Babban Birrnin Tarayya.


A ranar Alhamis kotun da ba da izinin bayan bukatar hakan da lauyan Emefiele, Mathew Bukka, SAN ya gabatar, yana neman ta sauya sharuddan belinsa da ta bayar.

A ranar 23 ga Nuwamba, 2023, Mai Shari’a Hamza Mu’azu ya ba da belin Emefiele, wanda Hukumar yaki da masu karya tattalin arzikin kasa (EFCC) ta gurfanar kan zargin badakalar biliyoyin kudade a lokacin shugabancinsa a CBN.

A lokacin, Mai Shari’a Hamza Mu’azu ya shardanta wa Emefiele ajiye kudi Naira miliyan 300 da kuma kawo mutum biyu wadanda kowannensu ya mallaki gida a unguwar Maitama a Abuja su tsaya masa.

Haka kuma alkalin ya shardanta wa tsohon gwamnan na CBN cewa ba zai fita daga Abuja zuwa wani waje ba.

Amma a zaman ranar Alhamis, lauyansa, Matthew Bukkak, ya bakaci a janye sharadrin hana shi fita daga Abuja, yana mai cewa a matsayin Emefiele na babban mutum, ba zai tsere ba idan aka yi masa sassaucin fita daga Abuja.

Lauyan ya kara da cewa hasali ma takardunsa na tafiye-tafiye suna hannun koutu don haka babu halin ya tsere.

Lauyan hukumar EFCC Rotimi Oyedepo, SAN, bai kalubanci bakutar lauyan na Emefiele ba, amma ya ce, “Duk da cewa takardun nasa suna hannun kotu, amma ya kamata ya rubuta alkawarin cewa ba zai bar Najeriya ba har sai an kammala shari’arsa.

“Wannan ba yana nufin cewa ina zargin sai iya tserewa,” in ji Oyedepo, wanda ya ce, “an sha samun wadanda takardunsu na tafiye-tafiye ke hannun kotun sun tsere daga Najeriya, inda suke zuwa su ba da takardar rantsuwar karya cewa takardun nasu sun bace.”

Bayan sauraron bangarorin, alkalin ya sahale wa Emefiele fita daga Abuja, bisa sharadin ya kasance a cikin Najeriya har sai an kammala shari’ar.

“Kotu ta amince da bukatar wanda ake zargi. Amma wajibi ne ya kasance a Najeriya har sai ab kammala shari’arsa,” in ji alkalin.

Thursday, 2 November 2023

Wike Yayi Alkawarin Kammala Gyaran Masallacin Kasa Da Cibiyar Yada Addinin Kirista Kan Lokaci

Mista Nyesom Wike, Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), ya yi alkawarin tabbatar da kammala aikin gyaran Masallacin kasa da cibiyar Kiristoci ta kasa da ke Abuja kan lokaci.

Wike ya ba da wannan tabbacin ne bayan ya duba aikin gyaran manyan gine-ginen kasa guda biyu a Abuja ranar Alhamis.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, NAN, ta tuno da cewa, shugabannin Masallacin kasa da Cibiyar Ibadar Kirista sun ziyarci Wike tare da rokon a kammala ayyukan gyara.

Wike, bayan ya tabbatar musu da cikakken goyon bayansa, ya yi alkawarin ziyartar cibiyoyin biyu domin ganin al'amura da kansa kafin ya yanke shawara kan mataki na gaba.

Ministan ya shaidawa manema labarai jim kadan bayan kammala rangadin aikin da aka gudanar a Masallacin kasa saboda karin aikin da ya kamata a yi.

Ya nuna jin dadinsa da abin da aka yi ya zuwa yanzu, ya kuma ba da izinin a saki kudi ga dan kwangilar domin samun damar kammala aikin.

A cibiyar kiristoci ta kasa, Wike ya ce zai duba kudin aikin gyaran kashi na biyu kuma zai amince da shi idan yana cikin abin da FCT za ta iya bayarwa.

Ya ce idan har kudin ya zarce matakin amincewa da babban birnin tarayya Abuja, zai tunkari Shugaba Bola Tinubu domin ya amince masa, inda ya tabbatar da cewa Tinubu ba zai yi watsi da irin wadannan muhimman abubuwan tarihi na kasa ba.

“Ba ya gaba da kowane addini; ya dauki dukkan addini a matsayin daya, domin mu Najeriya daya ce,” inji shi. (NAN)

Wednesday, 23 August 2023

Sunayen Unguwannin Da Wike Zai Yi Rusau A Abuja

Ministan Abuja, Nyesom Wike ya amince a rusa gine-gine sama da 6,000 a yankunan Garki da Jabi da wasu unguwanni 28 da suka saɓa da tsarin birnin tarayyan ba.

Hukumar kula da birnin tarayyar (FCTA) ta fitar da jerin sunayen unguwannin, inda ta bayyana cewa gine-ginen ta riga aka sanya wa alama ne rusau din zai shafa, a shirin gwamnati na kawar da gine-ginen da aka yi ba bisa ƙa’ida ba a birnin.

Ga jerin unguwannin da abin zai shafa:

Apo Mechanic Village
Byanzhin.
Dawaki.
Dai Dai.
Durumi.
Dutse.
Garki.
Garki Village.
Gishiri.
Gwagwalada.
Idu.
Jabi.
Kauyen Kado.
Karmo.
Karshi.
Karu.
Katampe.
Kauyen Ketti.
Kpaduma.
Kabusa.
Kauyen Kpana.
Kubwa.
Lokogoma.
Lugbe.
Mabushi.
Mpape.
Nyanya.
Piya Kasa.
Jikwoyi
Galadima
Tun ranar Litinin da aka rantsar da tsohon gwamnan na jihar Ribas a matsayin Minista, ya sha alwashin dawo da birnin kan ainihin taswirarsa, ruguza gine-ginen aka yi ba bisa tsaru ba, da kuma kawo karshen badaƙalar filaye a babban birnin.

Wike wanda ya ce ya zaga birnin Abuja a cikin dare domin ya ga al’amura da kansa, ya koka bisa yadda aka yi gine-gine a filayen da gwamnati ta kebe ba don ginawa ba.

Ya ce: “Za mu kwace duk filayen da masu su ba su gina ba, don haka dole masu su su ci gaba da aiki nan take.

Sai dai daraktan sashen kula da ci gaban FCTA, Muktar Galadima ya ce za a gudanar da wani sabon bincike.

(AMINIYA) 



Friday, 26 May 2023

Labari da dumiduminsa: Jirgin Nigeria Air Na Shirin Tashi Zuwa Abuja

A halin yanzu jirgin Najeriya Air wanda gwamnati ta dade tana alkawarin zai fara aiki, yana hanyarsa ta zuwa Abuja daga kasar waje
AMINIYA 

Sunday, 14 May 2023

’Yan Kasuwa 2 Sun Yi Kashin Kunshi 193 Na Hodar Iblis A Hannun NDLEA

Wasu ’yan kasuwa biyu sun yi kashin kunshi 193 na Hodar Iblis bayan shafe kwanaki uku a hannun jami’an Hukumar Yaki da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA).

Bayanai sun ce an cafke ababen zargin biyu ne a Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja, a ranar 10 ga watan Mayu yayin shigowarsu Najeriya daga kasar Uganda.

Haaland ya zama dan kwallon da babu kamarsa a Firimiyar Ingila a bana
Angola ta zarce Najeriya a hako danyen man fetur —OPEC
Mai Magana da Yawun NDLEA, Femi Babafemi ne ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a wannan Lahadin.

Mista Babafemi ya ce an dade ana neman mutanen biyu ruwa a jallo wadanda ake zargi ba su da wata sana’a face safarar miyagun kwayoyi.

Ya bayyana cewa bayan shafe kwanaki a hannun hukumar, daya daga cikinsu ya yi kashin kunshi 100 na Hodar Iblis wanda nauyinta ya kai kilo 2.137, yayin da abokin tafiyarsa ya yi kashin kunshi 93 na hodar mai nauyin kilo 1.986.

Kazalika, jami’an NDLEA sun kai samame wata mashayar miyagun kwayoyi a titin Bama da ke Sabon Gari da kuma Filin Wasa na Sani Abacha da ke birnin Kano, inda suka cafke ababen zargi 160 dauke da miyagun kwayoyi daban daban-daban.

Haka kuma, hukumar ta cafke wasu mutum biyu a titin Kano zuwa Maiduguri da tarin miyagun kwayoyi da suka hada da kwayoyi 5,000 na tramadol.

Wannan na zuwa ne a yayin da jami’an hukumar suka cafke wasu ababen zargi 25 a yankunan Tora Bora, Gwarinpa, Karmo, Kasuwar Garko, Bwari da sansanin ’yan gudun hijira na Kucigoro da ke Abuja.




Wednesday, 10 May 2023

Na Fi Karfin Kujerar Minista A Gwamnatin Tinibu - El-Rufa'i

 


Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya ce ba zai karba ba, ko an nada Ministan Babban Tarayya ba a Gwamnatin Bola Tinubu da za a rantsar ranar 29 ga wata Mayu da muke ciki.

Gwamnan ya yi wannan furucin ne a yayin da ake shirye-shiryen rabon mukamai a sabuwar gwamnatani, inda ake hasashen za a nada shi Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa ko kuma ministan Abuja.

“Ko an ba ni ministan Abuja ba zan karba ba. Na sha fada cewa ba na maimaita aji, kuma na san akwai matasan suka fi dacewa da kujerar,” in ji shi.

Da yake jawabi a wurin taron kaddamar da wani littafi a Abuja ranar Talata, ya bayyana cewa, “Ba zan koma gidan jiya ba. Kai! Tun da na bar Abuja ban sake komawa ba sai a 2016 da aka nada abokin karatuna a matsayin minista, ya bukaci gani na.

“Yanzu na tsufa da fita yin rusau, gara a samo matasa masu jini a jika.”

Ya ci gaba da cewa, “Nan da kwana 19 zan bar Kaduna, kuma ba zan kara zuwa ba sai idan ya zama dole. Ni ba na ma na ma tunanin kujerar ministan Abuja. Na gama da ita kuma ba zan ce komai kan ayyukan wadanda suka yi bayana ba.

El-Rufai, ya ce, wanda ke cikin mutanen da suka yi tsayuwar daka wajen ganin mulki ya koma yankin Arewa bayan wa’adin Shugaba Buhari — wanda hakan ya kai Tinubu ga nasara — ya ce ya fi karfin kujerar ministan.

A zamanin tsohon shugaban kasa Olusegun Obasanjo, gwamnan ya kasance ministan Abuja, inda ake ganin ya yi rawar gani wajen zamantar da birnin da kuma samar da cigaba.

AMINIYA

Thursday, 29 December 2022

Buhari Zai Sayo Motocin Sulke 400 Don Tsaron Su Abuja



Shugaba Buhari ya amince da sayo motocin sulke guda 400 don amfani da su wajen tabbatar da tsaro a babban birnin tarayya da jihohin Nasarawa da kuma Neja.

Sabon Kwamandan Rundunar Tsar Birgediya, Manjo-Janar Mohammed Usman ne ya bayyana hakan a ranar Laraba a jawabin godiyarsa a bikin nada masa anininsa bayan karin girma da ya samu.

Shugaban kasa tare da Babban Hafsan Sojin Kasa, Laftanar-Janar Faruk Yahaya da uwargidan kwamandan, Dokta Rekiya Usman, ne suka nada masa aninin.

Jim kadan bayan kammala bikin a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja, shugaban kasa ya bayyana shi a matsayin fitaccen jami’in da yake yi wa kasa hidima.

Buhari, a cikin wata sanarwa da hadiminsa, Garba Shehu ya fitar, ya yaba wa iyalan kwamandan bisa hakurin da suka yi na jure kalubalen da ya fuskanta wajen gudanar da aikinsa.

A nasa jawabin, Manjo-Janar Usman, ya gode wa shugaban kasa bisa irin gagarumin goyon bayan da ya bai wa Rundunar Sojin Najeriya, inda ya bayar da umarnin sayo motocin sulke guda 400.

A cewarsa, sun isa su tabbatar da tsaron yankin babban birnin tarayya, Nasarawa da sassan Jihar Neja.Ya bayyana farin cikinsa kan karin girma da aka yi masa, wanda ya ce  zai kara zaburar da shi wajen yin abin da ya dace game da nauyin da ya rataya a wuyansa.

(AMINIYA)


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...