Posts

Showing posts with the label Abuja

Kotu Ta Ba Emefiele Izinin Fita Daga Abuja

Image
  Kotu ta sahale wa tsohonn Gwamnan CBN, Godwin Emefiele, fita daga yankin Babban Birrnin Tarayya. Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta ba wa tsohonn Gwamnan Baban Bankin Najeriya (CBN) Godwin Emefiele, izinin fita daga yankin Babban Birrnin Tarayya. A ranar Alhamis kotun da ba da izinin bayan bukatar hakan da lauyan Emefiele, Mathew Bukka, SAN ya gabatar, yana neman ta sauya sharuddan belinsa da ta bayar. A ranar 23 ga Nuwamba, 2023, Mai Shari’a Hamza Mu’azu ya ba da belin Emefiele, wanda Hukumar yaki da masu karya tattalin arzikin kasa (EFCC) ta gurfanar kan zargin badakalar biliyoyin kudade a lokacin shugabancinsa a CBN. A lokacin, Mai Shari’a Hamza Mu’azu ya shardanta wa Emefiele ajiye kudi Naira miliyan 300 da kuma kawo mutum biyu wadanda kowannensu ya mallaki gida a unguwar Maitama a Abuja su tsaya masa. Haka kuma alkalin ya shardanta wa tsohon gwamnan na CBN cewa ba zai fita daga Abuja zuwa wani waje ba. Amma a zaman ranar Alhamis, lauyansa, Matthew Bukkak, ya bakaci a janye shar

Wike Yayi Alkawarin Kammala Gyaran Masallacin Kasa Da Cibiyar Yada Addinin Kirista Kan Lokaci

Image
Mista Nyesom Wike, Ministan Babban Birnin Tarayya (FCT), ya yi alkawarin tabbatar da kammala aikin gyaran Masallacin kasa da cibiyar Kiristoci ta kasa da ke Abuja kan lokaci. Wike ya ba da wannan tabbacin ne bayan ya duba aikin gyaran manyan gine-ginen kasa guda biyu a Abuja ranar Alhamis. Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya, NAN, ta tuno da cewa, shugabannin Masallacin kasa da Cibiyar Ibadar Kirista sun ziyarci Wike tare da rokon a kammala ayyukan gyara. Wike, bayan ya tabbatar musu da cikakken goyon bayansa, ya yi alkawarin ziyartar cibiyoyin biyu domin ganin al'amura da kansa kafin ya yanke shawara kan mataki na gaba. Ministan ya shaidawa manema labarai jim kadan bayan kammala rangadin aikin da aka gudanar a Masallacin kasa saboda karin aikin da ya kamata a yi. Ya nuna jin dadinsa da abin da aka yi ya zuwa yanzu, ya kuma ba da izinin a saki kudi ga dan kwangilar domin samun damar kammala aikin. A cibiyar kiristoci ta kasa, Wike ya ce zai duba kudin aikin gyaran ka

Sunayen Unguwannin Da Wike Zai Yi Rusau A Abuja

Image
Ministan Abuja, Nyesom Wike ya amince a rusa gine-gine sama da 6,000 a yankunan Garki da Jabi da wasu unguwanni 28 da suka saÉ“a da tsarin birnin tarayyan ba. Hukumar kula da birnin tarayyar (FCTA) ta fitar da jerin sunayen unguwannin, inda ta bayyana cewa gine-ginen ta riga aka sanya wa alama ne rusau din zai shafa, a shirin gwamnati na kawar da gine-ginen da aka yi ba bisa Æ™a’ida ba a birnin. Ga jerin unguwannin da abin zai shafa: Apo Mechanic Village Byanzhin. Dawaki. Dai Dai. Durumi. Dutse. Garki. Garki Village. Gishiri. Gwagwalada. Idu. Jabi. Kauyen Kado. Karmo. Karshi. Karu. Katampe. Kauyen Ketti. Kpaduma. Kabusa. Kauyen Kpana. Kubwa. Lokogoma. Lugbe. Mabushi. Mpape. Nyanya. Piya Kasa. Jikwoyi Galadima Tun ranar Litinin da aka rantsar da tsohon gwamnan na jihar Ribas a matsayin Minista, ya sha alwashin dawo da birnin kan ainihin taswirarsa, ruguza gine-ginen aka yi ba bisa tsaru ba, da kuma kawo karshen badaÆ™alar filaye a babban birnin. Wike wanda ya ce ya zaga birnin

Labari da dumiduminsa: Jirgin Nigeria Air Na Shirin Tashi Zuwa Abuja

Image
A halin yanzu jirgin Najeriya Air wanda gwamnati ta dade tana alkawarin zai fara aiki, yana hanyarsa ta zuwa Abuja daga kasar waje AMINIYA 

’Yan Kasuwa 2 Sun Yi Kashin Kunshi 193 Na Hodar Iblis A Hannun NDLEA

Image
Wasu ’yan kasuwa biyu sun yi kashin kunshi 193 na Hodar Iblis bayan shafe kwanaki uku a hannun jami’an Hukumar Yaki da Fataucin Miyagun Kwayoyi (NDLEA). Bayanai sun ce an cafke ababen zargin biyu ne a Filin Jirgin Sama na Nnamdi Azikiwe da ke Abuja, a ranar 10 ga watan Mayu yayin shigowarsu Najeriya daga kasar Uganda. Haaland ya zama dan kwallon da babu kamarsa a Firimiyar Ingila a bana Angola ta zarce Najeriya a hako danyen man fetur —OPEC Mai Magana da Yawun NDLEA, Femi Babafemi ne ya tabbatar da hakan cikin wata sanarwa da ya fitar a wannan Lahadin. Mista Babafemi ya ce an dade ana neman mutanen biyu ruwa a jallo wadanda ake zargi ba su da wata sana’a face safarar miyagun kwayoyi. Ya bayyana cewa bayan shafe kwanaki a hannun hukumar, daya daga cikinsu ya yi kashin kunshi 100 na Hodar Iblis wanda nauyinta ya kai kilo 2.137, yayin da abokin tafiyarsa ya yi kashin kunshi 93 na hodar mai nauyin kilo 1.986. Kazalika, jami’an NDLEA sun kai samame wata mashayar miyagun kwayoyi

Na Fi Karfin Kujerar Minista A Gwamnatin Tinibu - El-Rufa'i

Image
  Gwamnan Jihar Kaduna, Nasir El-Rufai ya ce ba zai karba ba, ko an nada Ministan Babban Tarayya ba a Gwamnatin Bola Tinubu da za a rantsar ranar 29 ga wata Mayu da muke ciki. Gwamnan ya yi wannan furucin ne a yayin da ake shirye-shiryen rabon mukamai a sabuwar gwamnatani, inda ake hasashen za a nada shi Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa ko kuma ministan Abuja. Yakin Sudan: Akwai yiwuwar maniyyata su kara biyan wasu kudin  DAGA LARABA: Zama Da Uwar Miji A Gida Daya: Inda Gizo Ke Saka “Ko an ba ni ministan Abuja ba zan karba ba. Na sha fada cewa ba na maimaita aji, kuma na san akwai matasan suka fi dacewa da kujerar,” in ji shi. Da yake jawabi a wurin taron kaddamar da wani littafi a Abuja ranar Talata, ya bayyana cewa, “Ba zan koma gidan jiya ba. Kai! Tun da na bar Abuja ban sake komawa ba sai a 2016 da aka nada abokin karatuna a matsayin minista, ya bukaci gani na. “Yanzu na tsufa da fita yin rusau, gara a samo matasa masu jini a jika.” Ya ci gaba da cewa, “Nan da kwana 19 zan b

Buhari Zai Sayo Motocin Sulke 400 Don Tsaron Su Abuja

Image
Shugaba Buhari ya amince da sayo motocin sulke guda 400 don amfani da su wajen tabbatar da tsaro a babban birnin tarayya da jihohin Nasarawa da kuma Neja. Sabon Kwamandan Rundunar Tsar Birgediya, Manjo-Janar Mohammed Usman ne ya bayyana hakan a ranar Laraba a jawabin godiyarsa a bikin nada masa anininsa bayan karin girma da ya samu. Shugaban kasa tare da Babban Hafsan Sojin Kasa, Laftanar-Janar Faruk Yahaya da uwargidan kwamandan, Dokta Rekiya Usman, ne suka nada masa aninin. Jim kadan bayan kammala bikin a Fadar Shugaban Kasa da ke Abuja, shugaban kasa ya bayyana shi a matsayin fitaccen jami’in da yake yi wa kasa hidima. Ya yaba wa Janar Usman bisa jajircewarsa da rikon amana da hakuri da kuma kwazo. Buhari, a cikin wata sanarwa da hadiminsa, Garba Shehu ya fitar, ya yaba wa iyalan kwamandan bisa hakurin da suka yi na jure kalubalen da ya fuskanta wajen gudanar da aikinsa. A nasa jawabin, Manjo-Janar Usman, ya gode wa shugaban kasa bisa irin gagarumin goyon bayan da ya bai wa Rundunar