Search This Blog

Showing posts with label Majalisar Dokoki. Show all posts
Showing posts with label Majalisar Dokoki. Show all posts

Tuesday, 21 April 2026

Gwamna Yusuf ya aika sunan Murtala Garo zuwa Majalisar Dokoki domin Tantance Shi A Matsayin Mataimakinsa

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya aika sunan Alhaji Murtala Sule Garo zuwa Majalisar Dokokin Jihar domin tantance shi tare da amincewa da shi a matsayin Mataimakin Gwamna.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yada Labaran Gwamnan, Mustapha Muhammad, ya sanya wa hannu.

Nadin ya yi daidai da Sashe na 191(3) na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima), wanda ke bai wa Gwamna damar nada Mataimakin Gwamna idan mukamin ya zama babu kowa a ciki.

Mukamin ya zama babu kowa ne bayan murabus din da tsohon Mataimakin Gwamna, Abdussalam Gwarzo, ya yi da kansa a ranar 27 ga Maris, 2026.

Bayan yin tuntuba mai fadi da masu ruwa da tsaki, Gwamnan ya bukaci Majalisar da ta amince da nadin Murtala Sule Garo.

Murtala Sule Garo mai shekaru 48, gogaggen dan siyasa ne kuma mai kwarewa a harkokin gudanarwa, inda ya shafe sama da shekaru ashirin yana rike mukamai daban-daban na zabe da na nada.

Ya taba zama Sakataren Tsare-tsare na jam’iyyarsa a jihar, Mashawarcin Gwamna na Musamman, da kuma zababben Shugaban Karamar Hukumar Kabo.

Haka kuma ya taba zama Shugaban ALGON a Kano, Kwamishinan Kananan Hukumomi da Harkokin Sarauta, da kuma dan takarar Mataimakin Gwamna na jam’iyyar APC a zaben 2023.

Nadin nasa wani bangare ne na kokarin kara inganta shugabanci da kuma dorewar kyakkyawan aikin yi wa al’umma hidima a Jihar Kano.

Tuesday, 21 May 2024

Majalisar Dokokin Kano Za Ta Yi Wa Dokar Masarautu Gyara

A shekarar 2019 dai aka yi wa dokar masarautu a jihar gyara inda aka ƙirƙiro ƙarin masarautu gudu huɗu masu daraja ta ɗaya a jihar.

Majalisar ta amince da hakan ne a zaman da ta yi na ranar Talata.

Majalisar Dokokin Kano  ta amince a dawo da dokar masarautu ta jihar domin yi mata kwaskwarima.

Majalisar ta amince da hakan ne a zaman da ta yi a ranar Talata.

A shekarar 2019 gwamnatin Abdullahi Umar Ganduje ta yi wa dokar masarautu ta jihar gyara inda aka ƙirƙiro ƙarin masarautu gudu huɗu masu daraja ta ɗaya.

Masarautun sun haɗa da Gaya da Ƙaraye da Rano waɗanda aka ɗaga darajarsu zuwa masu daraja da ta ɗaya daidai da masarautar Kano.

Sai kuma Masarautar Bichi da aka ƙirƙiro, abin da ya sa Kano ta zama tana da masarautu biyar masu daraja ta ɗaya.


Masu adawa da matakin a lokacin sun soki ƙirƙiro sababbin masarautu a Kano domin a cewarsu hakan zai rusa tarihin masaratuar Kano na daruruwan shekaru, inda masarautar take da ƙima a idon duniya saboda faɗinta da kuma tasirinta.

Amma mutanen yankunan da aka ƙirƙiro wa masarautun sun yi maraba da matakin, suna cewa hakan zai ƙara kawo musu ci gaba da bunƙasa.

(TRT Hausa)

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...