Posts

Showing posts with the label maniyyata

Hajj 2024: CBN Ya Janye Batun Biyan Kudin Guzurin Alhazai Ta Katin ATM

Image
Babban Bankin Najeriya ya dakatar da bayar da guzurin Alhazai na Hajji 2024 ta hanyar katin ATM Kwafin takardar da Bankin ya fitar wacce kuma  HAJJ REPORTERS ta gani mai kwanan wata 17 ga Mayu 2024 mai dauke da sa hannun daraktan riko na sashen ayyuka na kudi Solaja Muhammed J. Olawumi wanda aka aikewa bankunan kasuwanci ya ce “bayan gaggawar da aka samu tare da lura da karancin lokaci dangane da jigilar jirgin. Alhazan 2024, Shugabancin Bankin ya amince da biyan dukkanin tsabar kudi ga maniyyatan. “Ku lura cewa wannan sanarwar ta zarce tsarin da aka gabatar muku na farko na ayyukan Hajji na 2024. Nan ba da jimawa ba za a mika wata wasika a hukumance kan hakan.” Idan dai za a iya tunawa babban bankin ya sanar da hukumar alhazai ta kasa NAHCON da Jihohi da Rundunar Soji cewa za a biya kudin guzurin na Hajjin bana  wanda aka biya dala 500 ga kowane mahajjaci da kashi 60/40 cikin 100. tsabar kudi da kati Bankin ya ce dala 200 ne kawai za a ba da tsabar kudi yayin da za a ba da

Hajj2024: Anyi Kira Ga Kason Farko Na Maniyyatan Bauchi Su Kasance Jakadun Jahar Nagari

Image
Amirul Hajj 2024 ma jahar Bauchi, ya bukaci alhazan jihar da su kasance jakadu nagari tare da nuna biyayya da mutunta ka’idojin da Saudiyya ta shimfida. A sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Muhammad Sani Yunusa ya sanyawa hannu, yace Amirul hajj wanda kuma ya kasance Mai Martaba Sarkin Dass Alh. Usman Bilyaminu Othman ya yi wannan nasihar ne a wajen bankwana na musamman ga rukunin farko na maniyyata da aka gudanar a filin jirgin saman Sir Abubakar Tafawa Balew Sarkin Dass ya bayyana cewa jajircewar da gwamnatin Gwamna Bala Abdulkadir ta yi kan al’amuran addini alama ce da ke nuna sha’awar sa ga rayuwar al’umma. A lokacin da yake yi musu fatan  yin Hajji karbabbiya, Amirul hajj din ya bukaci maniyyatan da ke da damar zuwa aikin hajjin bana da su yi wa Gwamna addu’a. Jihar Bauchi da kasa baki daya. A nasa jawabin shugaban kwamitin yada labarai na tawagar Amerul hajji Alh. Yayanuwa Zainabari ya bayyana yadda aikin ya gudana cikin sauki, inda ya

Hajj 2024: Kungiyar Fararen Hula Ta Yi Kira Ga Babban Bankin Najeriya Ya Sauya Tunani Kan Biyan Kudin Guzurin Alhazai

Image
An shawarci Babban Bankin Najeriya (CBN) da ya yi watsi da ra’ayin bayar da kudin  (BTA) ta hanyar katin biyan kudi. Kungiyar fararen hula masu daukar rahotannin aikin Hajji  (IHR) ne suka bayar da wannan shawarar a wata sanarwa da babban jami'inta na kasa Ibrahim Mohammed ya fitar. Kungiyar ta ce kasa da sa’o’i 24 da fara jigilar maniyyata zuwa kasa mai tsarki, babban Bankin ya umarci wasu bankunan kasuwanci da su biya maniyyatan dala 200 kacal daga cikin dala 500 da ake sa ran kowane mahajjaci zai samu yayin da sauran dala 300. za a bayar a kan katin cirar kudi  “Alhazai na bana sun riga sun shiga cikin rashin tabbas da yawa tun daga manufofin sayayya da suka haifar da hauhawar farashin Hajji zuwa raguwar kudin guzuri. Wannan shawarar da babban bankin ya yanke zai kara musu bala’i ne kawai”. “ Sanin kowa ne cewa mafi yawan alhazanmu sun fito ne daga karkara kuma ba su da masaniyar harkar hada-hadar kudi, yawancin ma ba su san yadda ake amfani da katin ATM ba.  Har

Hajin 2024: Hukumar Alhazai Ta Bauchi Ta Bayyana Farin Cikinta Bisa Yadda Maniyyata Suka Je Asibitoci Domin Yi Musu Rigakafi

Image
Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Bauchi ta bayyana jin dadinta kan yadda maniyya suka fita domin karbar allurar rigakafi A sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Muhammad Sani Yunusa ya sanyawa hannu, yace Sakataren zartarwa na hukumar limamin Abdurrahman Ibrahim Idris ya bayyana haka a lokacin da yake karbar rahoton aikin rigakafin da ake yi daga kananan hukumomin jihar 20. Ya ce an fara gudanar da aikin ne a jiya Lahadi 11 ga watan Mayu, 2024 tare da maniyyatan karamar hukumar Bauchi da sauran kananan hukumomin da ke kusa da babban birnin jihar kamar Dass, Tafawa Balewa, Bogoro, Alkaleri, Kirfi da Ganjuwa Imam Abdurrahman ya kara da cewa maniyyatan wadanda ke nesa na kananan hukumomin Katagum, Gamawa da. Zaki, sun fita da yawa zuwa manyan asibitocinsu daban-daban domin ayi musu rigakafin, yana mai bayyana yadda lamarin ya kasance abin karfafa gwiwa. Don haka yay Kira ga maniyyatan da har yanzu ba a yi musu allurar ba da su yi hak

Hajjin 2024: Sakataren Hukumar Alhazai Na Bauchi Bayyana Muhimmancin Yi Wa Maniyyata Rigakafi

Image
Sakataren Zartarwa na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Bauchi Imam Abdurrahman Ibrahim Idris ya bayyana jin dadinsa da tsare-tsaren Hukumar Kula da Lafiya a matakin farko ta jiha na fara gudanar da allurar rigakafin cututtukan da za a iya kauce musu kamar su diphtheria, polio da kyanda.  A sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Muhammad Sani Yunusa ya sanyawa hannu, yace Imam Abdurrahman ya bayyana jin dadinsa a lokacin da ya ziyarci wajen ajiye magunguna na jihar da ke asibitin kwararru na Bauchi, a fadar jiha.  Ya bayyana cewa ya je gurin ajiyar ne domin ganewa idonsa shirye-shiryen hukumar lafiya matakin farko na jihar gabanin gudanar da allurar rigakafin cutar a fadin jihar. Babban sakataren wanda ya nuna farin cikinsa kan abin da ya gani a gurin ajiye magungunan, ya yi nadamar sanar da rashin fara aikin rigakafin a yau kamar yadda aka tsara tun da farko, a cewarsa, sakamakon cikas da aka samu ne wajen kawo maganin a jiha.    Ya bayyana wasu ’yan sau

Shugaban NAHCON Ya Yabawa Gwamnan Imo Bisa Tallafawa Maniyyatan Jahar

Image
Hukumar alhazai ta kasa NAHCON a yau ta karbi bakuncin gwamnan jihar Imo, Hope Uzodinma, wanda ya kai ziyarar ban girma a gidan alhazai dake Abuja. A sanarwar da mataimakin daraktan yada labarai na hukumar, Mousa Ubandawaki ya sanyawa hannu, yace A jawabinsa na maraba, Malam Jalal Ahmad Arabi ya bayyana jin dadinsa da karbar bakuncin Gwamnan Jihar Imo a gidan Hajji. Arabi ya bayyana Gwamna Uzodinma a matsayin wani ginshikin tallafi ga Hukumar tare da bayyana yadda ya yi kokarin ganin alhazan jihar sa da ke da niyyar shiga aikin Hajjin bana. A cewarsa, “Kun kasance ginshikin goyon bayanmu a Hukumar ta hanyar goyon bayanku na ganin cewa Musulmin Jihar Imo sun samu damar shiga aikin Hajji. Kun tallafa mana a 2023 da ma bana duk da kasancewar kiristanci ne kuma jihar Imo jihar ce mafi rinjayen Kirista. A gare mu ku alama ce ta zaman lafiya tare da addini da hadin kai a kasar." Ya kuma baiwa Gwamna Hope Uzodinma takardar yabo da lambar yabo ta 🥈 f nagari bisa goyon bayansa

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano Ta Kammala Shirye-Shiryen Aikin Hajjin 2024 - Laminu Rabi'u Danbappa

Image
Shugaban Hukumar Kula da Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Yusif Lawan, ya bayyana a yau Laraba cewa sun samu nasarar kammala dukkan shirye-shiryen aikin hajjin 2024 a kasar Saudiyya. A sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Sulaiman Abdullahi Dederi ya sanyawa hannu, yace Wannan sanarwar ta zo ne a yayin gabatar da kayayyakin bulaguro bayan taron hukumar da aka gudanar a dakin taro. Alhaji Yusif Lawan ya jaddada kudirin hukumar na ganin an shirya tsaf da kuma tashi zuwa aikin hajjin a kan kari, sakamakon tsare-tsaren masu inganci da suka yi. An kula da kowane fanni na aikin hajji, tun daga kaya na hannu zuwa inufom din maza da mata, da hijabi na alhazai mata, da littafan jagororin aikin Hajji, wanda hakan ya baiwa alhazan Kano damar gudanar da tafiyarsu ta alfarma da kwarin gwiwa da kwanciyar hankali. A nasa jawabin Darakta Janar na hukumar jin dadin alhazai ta jihar Kano, Alhaji Laminu Rabi’u Danbappa ya yabawa shuwagabannin da suka sa i

Jinkirin Mika Fasfon Maniyyata Na Kawo Cikas Ga Aikin Yin Bizar Aikin Hajji - Laminu Rabi'u

Image
Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Laminu Rabi’u Danbappa, ya bayyana  jinkirin mika fasfo  ga hukumar a matsayin  babban kalubalen da ke kawo cikas wajen yin Bizar aikin Hajji ga maniyyata Yayin wata ziyara zuwa daya daga cikin cibiyoyin bitar Alhazai  da aka gudanar a karamar hukumar Doguwa a yau, Alhaji Laminu Rabi’u Danbappa ya jaddada muhimmancin bayar da fasfo a kan lokaci wajen saukaka gudanar da bizar aikin Hajji cikin sauki ga maniyyata. A cikin sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Sulaiman Abdullahi Dederi ya sanyawa hannu, yace Alhaji Danbappa, wanda wakilin hukumar gudanarwa na hukumar, Malam Ismail Mangu ya wakilta, ya bayyana cewa, “jinkirin tura fasfo na kasa da kasa yana kawo cikas wajen gudanar da aikin Hajji yadda ya kamata ga maniyyatan mu, ya zama wajibi mu daidaita wannan aiki domin tabbatar da kammala aikin a kan lokaci. da kuma inganta aikin hajji gaba daya”. Malam Ismail Mangu ya kara jaddada muhimmanc

Har Yanzu 29 Ga Watan Afurilu Ce Ranar Karshe Ta Rufe Yin Bizar Hajin 2024 - Laminu Rabi'u Danbaffa

Image
Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Laminu Rabi’u Danbappa ne ya bayyana hakan a yau yayin liyafar cin nasara a kotun koli da jami’an hukumar alhazai 44 suka shirya cewa masarautar Saudiyya ta tsaya tsayin daka kan dokokin aikin Hajji na shekarar 2024.  A sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Sulaiman Abdullahi Dederi ya sanyawa hannu, yace Alhaji Laminu Rabi’u Danbappa ya bukaci jami’an cibiyar Hajji da su rika fadakar da al’umma wannan wa’adin don tabbatar da cewa ba a bar wani mahajjaci a baya ba. Da yake jawabi kan liyafar da aka karrama Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusif, Alhaji Laminu Rabi’u Danbappa ya bayyana cewa, wannan shi ne mataki na farko, kuma ana sa ran za a samu ci gaba.  Ya kuma roki Allah Madaukakin Sarki da Ya yi wa Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusif jagora ya kuma kare shi a dukkan al’amuransa. A nasa jawabin shugaban kungiyar Jami'an Alhazai na kananan hukumomi na Jahar Kano wanda kuma ya kasance jami’in Alhaz

Zamu Iya Kwatanta Farin Cikinmu Ne Kadai Da Shiga Aljanna- Inji Mahajjatan Najeriyan Da Suka Je Hajji A Karon Farko

Image
Wata alhajiyar Najeriya, Hauwa’u Sa’ad Joda ta ce shiga aljanna ne kawai zai fi dadi fiye da jin dadin da take ji a halin yanzu yayin da take kasar Saudiyya don gudanar da aikin Hajjin 2023. A tattaunawar da Jaridar Hajj Reporters ta yi da Joda, wata alhaji daga jihar Adamawa, ita ma ta ce ba za ta iya bayyana yadda take ji ba saboda burinta na rayuwa ya cika. Da take zantawa da manema labarai a ziyarar da ta kai garin Uhud daya daga cikin wuraren da mahajjata suka ziyarta don ganin wasu wuraren tarihi, Hajiya Joda ta bayyana cewa ‘yar uwarta Aisha Ahmad ce ta dauki nauyin gudanar da aikin Hajjin. A cewarta, ta kasa danne kukanta a lokacin da ’yar’uwar ta sanar da ita batun zuwa aikin Hajjin bana, inda ta bayyana cewa “ba za a iya misalta abin farin cikin ba saboda burina na rayuwa ya cika.” Da aka tambaye ta game da ayyukan da Hukumar Alhazai ta Jihar Adamawa da Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON suka yi mata daga Najeriya zuwa Saudiyya,  Joda ta ce komai ya tafi cikin nas

Hajj2023 : Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Yi Ban Kwana Da Maniyyatan Kano 'Yan Jirgi Na Farko

Image
A yayin da ake shirye-shiryen gudanar da aikin hajjin bana, Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir ya yi bankwana da kashin farko na maniyyata 555 da suka tashi daga filin jirgin saman Malam Aminu Kano (MAKIA) zuwa kasar Saudiyya a cikin jirgin Max Air. jirgin sama Boeing 747. A sanarwar da babban sakataren yada labaran Gwaman Sunusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu, Da yake jawabi ga maniyyatan da suke shirin tashi, Gwamnan ya taya su murna da yardan Allah da samun damar sauke nauyin da ya wajaba a kan kowane Musulmin da ya cancanta sau daya a rayuwarsa tare da yi musu nasiha. “Ina so in yi amfani da wannan dama domin taya ku murna a matsayinku na rukunin farko na mahajjatanmu da wadanda suka amsa kiran Allah SWT na cika daya daga cikin ibadun da suka wajaba. Ina so a madadin gwamnati da na jihar Kano ina kira gare ku da ku zama jakadu nagari a jihar, kuma ku nisanta kanku daga duk wani nau'i na miyagun laifuka kamar safarar muggan kwayoyi, fashi da makami, zanga-z

Ba Mu Yi Wa Alhazai Karin Wajibi A Kudin Aikin Hajji Ba - NAHCON

Image
Hukumar Alhazai ta Najeriya NAHCON ta sanar da wani labari da ke ci gaba da yaduwa ko kuma bayanin cewa an umurci maniyyata aikin Hajjin bana da su biya karin Dala 100 ta Amurka  A sanarwar da mataimakin daraktan harkokin yada labarai da dab'i na hukumar, Mousa Ubandawaki ya fitar, yace, yana da kyau a fayyace cewa rikicin Sudan wanda ya janyo rufe sararin samaniyarta saboda dalilai na tsaro. Sakamakon haka, dukkan jiragen Alhazan za su yi tafiya ta hanyoyi daban-daban wadanda ke da tsawon awa 1 da mintuna 40 zuwa awa 3 dangane da wuraren tashi a Najeriya. Wannan hanya ta dabam za ta tilasta masu jigilar alhazai su bi ta sararin samaniyar Cameroun, Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya (CAR), Uganda, Kenya, Habasha da Eritrea, tare da Æ™arin farashin man jiragen sama da kuma kuÉ—in jirgi. Mun yi nazari sosai kan duk hanyoyin da za a bi don samar da Æ™arin dala 250 ga kamfanonin jiragen sama waÉ—anda suka haÉ—a da tsari da tarurruka da kamfanonin jiragen sama, Hukumar Kula da Sufurin

Karin Kudin Tikiti: Za A Dauki Dala 100 Daga Guzurin Alhazai

Image
  Hukumar Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta ce za ta dauki Dala 100 daga cikin kudin guzurin maniyyata aikin Hajjin bana, domin biyan karin kudin kujera da kamfanonin jiragen da za su yi jigilar su suka yi.  Yakin da ake yi a Sudan ya sa kasar rufe sararin samaniyarta, don haka dole sai jiragen da za su dauki maniyyatan su bi sabuwar hanya da ta bi ta kasar Chadi da Habasha da Eretiyiya da Kamaru kafin isa kasar Saudiyya. ِKafin barkewar yakin da ya sa aka rufe sararin samaniyyan Sudan, jiragen maniyyatan Najeriya kan tsallaka ne ta Chadi su shiga Sudan ne kadai kafin su isa Saudiyya. Wani manaja a wani kamfanin da zai yi jigilar alhazan ya bayyana wa Aminiya cewa, “A duk lokacin da aka tsayin tafiya ya karu to dole kudi su karu saboda man da za a zuba a jirgi ya karu, haka kuma kudin da za a biya ma’aikatan jirgi shi ma ya karu; Hakan ya janyo dole a yi kari a kudin tikitin alhazan.” Bayan yamutsa gashin baki da kai-kawo a tsakanin Hukumar NAHCON da kamfanonin jiragen a kan karin kudin,

Hajj2023: Duk Karin Da Aka Samu A Kudin Aikin Hajin Bana, Babu Maniyyacin Da Za Ce Ya Sake Biya- Shugaban NAHCON

Image
Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON) ta bayyana cewa, duk da karin dalar Amurka kusan $313 (N141, 476) kan kudin aikin hajjin bana, hukumar ba za ta nemi maniyyatan su sake biyan wasu kudade ba. Shugaban Hukumar NAHCON, Zikirullah Kunle Hassan, ya bayyana hakan ne a lokacin da yake gabatar da jawabin bude taron bita na yini daya ga jami’an Hajji da ma’aikatar Hajji da Umrah ta Saudiyya ta shirya, wanda aka gudanar a gidan Hajji da ke Abuja a ranar Asabar din da ta gabata bayan barkewar rikici a kasar Sudan da kuma ‘yan gudun hijira. rufe sararin samaniyarsa, kamfanonin jiragen saman Najeriya hudu da aka zaba don aikin Hajjin 2023 sun bukaci hukumar da ta ba ta dala 250 tikitin jirgin kowane mahajjaci.   Alhaji Hassan ya kuma ce hukumar a ranar 6 ga watan Mayu, ta gano cewa akwai Æ™arin kudaden aiki guda biyu na dalar Amurka 63 daga Saudi Arabiya wanda ba a sanyasu ba a tattaunawar da aka yi tun farko gabanin sanar da farashin farashi na Æ™arshe. Ya ce tuni NAHCON ta rubutawa ma’a

Yakin Sudan: Akwai Yiwuwar Maniyyata Su Kara Biyan Wasu Kudin

Image
  Hukumar Aikin Hajji ta Kasa (NAHCON) ta tabbatar da cewa yaÆ™in da ake yi a kasar Sudan zai shafi jigilar maniyyatan Najeriya na bana, wanda ka iya sanadin karin kudin kujerar. A ranar Talata hukumar da kamfanonin sufurin jiragen sama na cikin gida suka rattaba hannu a kan yarjejeniyar jigilar mahajjatan ta bana A makon jiya dai sun gaza yin hakan saboda batun Æ™arin kuÉ—i. Sai dai hukumar ba ta bayyana ko matakin na nufin, maniyyata aikin hajji ne za su biya Æ™arin kuÉ—in da dogon zagayen zuwa kasa mai tsarki ko a’a ba. Kwamishinan Tsare-tsare da Gudanar da Gikin Hajji a hukumar, Abdullahi Magaji Hardawa, ya ce har zuwa yanzu ba a cimma matsaya kan ko mahajjata ne za su yi Æ™arin kuÉ—in ba. A cewarsa, matuÆ™ar ba a buÉ—e sararin samaniyar kasar Sudan ba, har aka fara jigilar maniyyatan bana daga Najeriya, to dole sai jiragen sama sun yi zagaye, wanda zai haddasa Æ™arin kuÉ—i. Jami’in ya ce babban hatsari ne jirgin sama ya ratsa ta sararin samaniyar Sudan, shi ya sa hukumomin Æ™asar suka dakatar

#hajj2023 Hukumar alhazai ta Kano, ta yi kira ga duk mai niyyar zuwa Hajin bana, da ya gaggauta biya

Image