Posts

Showing posts with the label Layin man fetur

An fara cinkoson sayen fetur a Lagos sakamakon kalaman Tinubu

Image
An fara dogayen layuka a gidajen sayar da man fetur da ke birnin Lagos na Najeriya jim kadan da sanarwar da shugaban kasar, Bola Ahmed Tinubu ya yi ta janye kudin tallafin man fetur. An fara cinkoson sayen fetur a Lagos sakamakon kalaman Tinubu An fara dogayen layuka a gidajen sayar da man fetur da ke birnin Lagos na Najeriya jim kadan da sanarwar da shugaban kasar, Bola Ahmed Tinubu ya yi ta janye kudin tallafin man fetur. Jaridar Daily Trust ta rawaito cewa, direbobin motoci sun yi cincirindo a gidajen mai na NNPC da ke Ikeja, inda suke rige-rigen sayen man. Jaridar ta rawaito cewa, da dama daga cikin gidajen man fetur masu zaman kansu ba sa sayar da man ya zuwa lokacin da Daily Trust ta fitar da rahoton. A yayin gabatar da jawabinsa na shan rantsuwar kama aiki a yau Litinin, shugaba Tinubu ya bayyana cewa, mawadata ne kadai ke amfana da kudin tallafin man fetur din a maimakon talakawa. Tinubu ya ce, gwamnatinsa za ta karkatar da kudin tallafin zuwa ga bangarorin ilimi da