Search This Blog

Showing posts with label Katin zabe. Show all posts
Showing posts with label Katin zabe. Show all posts

Friday, 13 January 2023

Sabbin Katinan Zabe 13m Muka Buga —INEC


Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) na bincike kan zargin jami’anta da karbar na goro a aikin rabon katin zabe da ke gudana.

Hukumar ta kara da cewa ta buga sabbin katinan zabe miliyan 13 da dubu 868 da 441 bayan kammala aikin rajistar sabbin masu zabe.

Da yake sanar da hakan, Kwamishinan INEC na Kasa kan Wayar da Masu Zabe da Yada Labarai, Festus Okoye, ya ce, “Hukumar ta damu bayan samun korafe-korafe kan nuna fifiko a wasu wuraren rabon katin.

“Duk halastattun masu rajista na da ’yancin karbar katinsu domin kada kuri’a a ranar zabe a wuraren da suka yi rajista.”

“Domin kawar da shakku, sabbin katunan zabe miliyan 3 da dubu 868 da 441 INEC ta buga da suka hada da na sabbin wadanda suka yi rajista da wadanda suka sauya wurin zabe da kuma wadanda aka sabunta katinsu.”

Okoye ya sanar cewa hukumar ta kara lokacin rabon katin zuwa ranar 29 ga watan Janairu da muke ciki, daga karfe 9 na safe zuwa 3 na rana, har da ranakun Asabar da Lahadi.

Hukumar ta kuma umarci jami’anta masu aikin rabon katin da su tattara duk wani korafi rashin buga kati zuwa ga shugabanninsu a jihohi domin daukar matakin da ya dace.

(AMINIYA)

Thursday, 12 January 2023

LABARI DA DUMIDUMINSA! INEC ta kara wa’adin lokacin Karbar katin zabe

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta kara wa’adin da ta sanar na kammala rabon katin zabe da mako guda a fadin Najeriya.

Karin bayani na tafe

Wednesday, 4 January 2023

Duk wanda ba shi da kuri'a ba zai yi zabe ba - INEC


Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa ta jaddada cewa babu wanda zai kada kuri'a a zaben 2023 mai zuwa sai mai katin zabe 

Jami'in zabe na karamar hukumar Gwarzo Mal.Bello Ismail ya bayyana haka a lokacin taron masu ruwa da tsaki a ofishinsa. 

Bello Ismail ya kara da cewa an samar da sabbin rumfuna saba'in da uku domin rage cinkoso da masu kada kuri'a sama da dubu daya a Gwarzo,Getso,Kutama,Lakwaya,Mada da ,Unguwar tudu dake karamar hukumar Gwarzo.

 Jami’in zaben ya kuma kara da cewa INEC za ta kai unguwanni goma na kananan hukumomin domin rabon kaya daga ranar 6 ga watan Janairu zuwa 15 ga watan Janairu.

Da yake jawabi a wajen taron sakataren jam’iyyar A.P.C. Samaila Abdullahi ya shawarci hukumar zabe da ta kaucewa tarin pVC na uku.

A nasu jawabin jami'in 'yan sanda DSS, da Civil Defence kira suka yi INEC da su bayar da motocin daukar kayan zabe da jami’ai domin kaisu wuraren da ya dace. 

Sauran wadanda suka halarci taron sun hada da wakilan babban limami, hakimin gundumar, shugabannin jam'iyya da dai sauransu.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...