Search This Blog

Showing posts with label Gidan marayu. Show all posts
Showing posts with label Gidan marayu. Show all posts

Tuesday, 17 January 2023

Gwamnatin Kano ta kori 'yan mata biyu daga gidan marayu kan zargin tayar da husuma

Hukumomi a jihar Kano ta kori wasu 'yan mata daga gidan marayu na gwamnatin jihar.

Gwamnatin ta ce ta ɗauki matakin ne saboda 'yan matan ba sa bin ƙa'idar zaman gidan tare da ƙoƙarin tayar da husuma tsakanin marayu da ma’aikata.

Sai dai marayun sun ce wasu ma’aikatan gidan ne ke cin zarafinsu ta hanyar ƙoƙarin yin lalata da wasu daga cikinsu.

Ma’aikatar harkokin mata da walwalar al‘ummar ta jihar Kano, ta ce ta kori ‘yan matan biyu daga gidan marayun na Nasarawa ne saboda rashin kiyaye ka’idoji da dokokin zaman gidan.

Sai dai waɗannan ‘yan mata sun ce saboda sun kwarmata lalatar da ake zargin wani ma’aikacin gidan ne ya sa aka kore su, kamar yadda ɗaya daga cikinsu ta shaida wa Majiyarmu 

Ta ce ''saboda yana da mabuɗin sito a hannansa, yana ganin kamar shi ke da iko da gidan gaba ɗaya, sai muka je muka gaya wa shugabar gidan, daga baya sai ta zo ta ce ai mun yi masa ƙazafi, daga sai suka rubuta takarda suka kai wa Kwamishina, ita kuma ta bayar da umarnin da a rubuta takarda wai an kore mu, daga baya aka zo aka kira mu aka yi mana wa'azi, cewa mu yadda da ƙaddara mai kyau da marar kyau''

Daga nan sai a ka sanar da su cewa gwamna ya bayar da umarni a kore su daga gidan tun da za su janyo masa matsala kamar yadda ta shaida wa majiyarmu .

Ta ƙara da cewa ''mun ɗauki matakin bayyana abin da ma'aikacin gidan ke yi wa 'yan matan da ke gidan ne, saboda 'yan matan da yake lalata da su 'yan uwanmu ne, dan haka bai makata mu yi shiru ba''

Dan haka a cewarsu bai makata a ajiye ma'aikaci ba amma kuma ya riƙa cin amanar yara da gwamnati.

Daga ƙarshe 'yan matan sun yi kira ga gwamnati da ta shiga cikin lamarin tare da taimaka wa wajen samar musu da wurin zama.

Haka kuma 'yan matan sun ƙaryata batun zargin da ake yi musu na tunzura sauran yara da kuma fita daga gidan kuma ba sa dawowa sai lokacin da suka ga dama, domin kuwa a cewarsu suna zaman lafiya da sauran yaran.
(BBC HAUSA) 

Gwamnatin Kano Ta Musanta Cin Zarafin Yara A Gidan Marayu

 


Gwamnatin Jihar Kano ta yi watsi da rahoton zargin cin zarafin yara da wasu jami’anta suka yi a gidan marayu da ke Nassarawa a jihar.

Kwamishinar Harkokin Mata da Ci Gaban Al’umma ta jihar, Dakta Zahra’u Muhammad Umar, ta yi watsi da rahoton yayin da ta zanta da manema labarai a ranar 

“Wasu masu yin barna ne suka hada labarin don bata sunan gwamnatin jihar nan.

“Amma abin da ta faru shi ne ba mu da hurumin ci gaba da zama da kuma kulawa da yaran da suka haura shekara 18 a gidan marayu. Doka ma ba ta ba mu wannan damar ba.“An bukaci wasu mutum biyu, Ladidi da Saudat da su bar gidan marayun tun da yanzu sun zama manya.”

Jaridar Aminiya ta rawaito cewa kwamishinar Ta bayyana cewa matan biyu, wadda daya daga ciki bazawara ce, dayar kuma na da aure har da ’ya’ya uku, sun ki barin gidan sannan sun shiga yi wa kwamishinar bita da kulli da sauran ma’aikatan don bata musu suna.

“Sun shiga gidan rediyon sun yi kazafin cewar ana cin zarafin yara, ana kai su wurare daban-daban ba bisa ka’ida ba.”Ta ce gwamnatin jihar ta kafa wani kwamiti wanda ya gudanar da bincike sannan ya gano zargin karya ne, inda ta ce kwamitin ya yanke shawarar cewa Ladidi da Saudat su bar gidan saboda sun haura shekara 30.“Lokacin da na zama kwamishina, na tausaya wa manya, na zama uwa gare su, na sanya wasu daga cikinsu a manyan makarantu.”

Ta ce gwamnatin jihar ba za ta yi kasa a gwiwa ba a kokarinta na daukaka darajar rayuwa a tsakanin ‘yan kasa ta hanyar manufofi da tsare-tsare.

A nasa bangaren, shugaban kwamitin binciken, Alhaji Kabiru Zubairu, ya ce kwamitin da gwamnatin jihar ta kafa ya kunshi mambobi tara da za su kula da yadda ake kulawa da marayun.

Kwamitin ya hada da Jami’in ‘yan Sanda a matsayin Sakatare, REPA, Darakta (Yaron Ma’aikatar), Masanin Ilimi daga Ma’aikatar Ilimi, Jami’in Shari’a, Likita da Jami’an Jin Dadin Jama’a a matsayin mambobi.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...