Posts

Showing posts with the label Gidan marayu

Gwamnatin Kano ta kori 'yan mata biyu daga gidan marayu kan zargin tayar da husuma

Image
Hukumomi a jihar Kano ta kori wasu 'yan mata daga gidan marayu na gwamnatin jihar. Gwamnatin ta ce ta ɗauki matakin ne saboda 'yan matan ba sa bin ƙa'idar zaman gidan tare da ƙoƙarin tayar da husuma tsakanin marayu da ma’aikata. Sai dai marayun sun ce wasu ma’aikatan gidan ne ke cin zarafinsu ta hanyar ƙoƙarin yin lalata da wasu daga cikinsu. Ma’aikatar harkokin mata da walwalar al‘ummar ta jihar Kano, ta ce ta kori ‘yan matan biyu daga gidan marayun na Nasarawa ne saboda rashin kiyaye ka’idoji da dokokin zaman gidan. Sai dai waɗannan ‘yan mata sun ce saboda sun kwarmata lalatar da ake zargin wani ma’aikacin gidan ne ya sa aka kore su, kamar yadda ɗaya daga cikinsu ta shaida wa Majiyarmu  Ta ce ''saboda yana da mabuɗin sito a hannansa, yana ganin kamar shi ke da iko da gidan gaba ɗaya, sai muka je muka gaya wa shugabar gidan, daga baya sai ta zo ta ce ai mun yi masa ƙazafi, daga sai suka rubuta takarda suka kai wa Kwamishina, ita kuma ta bayar da umarnin

Gwamnatin Kano Ta Musanta Cin Zarafin Yara A Gidan Marayu

Image
  Gwamnatin Jihar Kano ta yi watsi da rahoton zargin cin zarafin yara da wasu jami’anta suka yi a gidan marayu da ke Nassarawa a jihar. Kwamishinar Harkokin Mata da Ci Gaban Al’umma ta jihar, Dakta Zahra’u Muhammad Umar, ta yi watsi da rahoton yayin da ta zanta da manema labarai a ranar  “Wasu masu yin barna ne suka hada labarin don bata sunan gwamnatin jihar nan. “Amma abin da ta faru shi ne ba mu da hurumin ci gaba da zama da kuma kulawa da yaran da suka haura shekara 18 a gidan marayu. Doka ma ba ta ba mu wannan damar ba. “An bukaci wasu mutum biyu, Ladidi da Saudat da su bar gidan marayun tun da yanzu sun zama manya.” Jaridar Aminiya ta rawaito cewa kwamishinar Ta bayyana cewa matan biyu, wadda daya daga ciki bazawara ce, dayar kuma na da aure har da ’ya’ya uku, sun ki barin gidan sannan sun shiga yi wa kwamishinar bita da kulli da sauran ma’aikatan don bata musu suna. “Sun shiga gidan rediyon sun yi kazafin cewar ana cin zarafin yara, ana kai su wurare daban-daban ba bisa ka’ida b