Search This Blog

Showing posts with label SIyasar Kano. Show all posts
Showing posts with label SIyasar Kano. Show all posts

Saturday, 23 September 2023

Darussa Daga Siyasar Kano Ta 2023 - Dr Sa'idu Ahmad Dukawa

Tun lokacin da Injiniya Abba Kabir Yusuf ya zama gwamnan Kano daga zaben da aka gudanar a watan Maris na wannan shekarar (ta 2023) har izuwa ranar Laraba, 20/9/23, siyasar Kano (wacce ake yiwa taken “sai Kano!”) ta dada zafafa fiye da ko da yaushe a wannan zubin dimokaradiyyar (ta Jamhuriya ta hudu). A bisa fahimtata, dalilai kamar shida ne suka janyo haka. 

Za mu yi bitarsu a takaice domin amfanin gaba.

1. Zafin hamaiyar siyasa tsakanin Senator Rabiu Musa Kwankwaso da Dr. Abdullahi Umar Ganduje. Wannan ta sa wadannan jagororin na Kano guda biyu sun fifita bukatun kansu, na neman wani ya ga bayan wani a siyasance, fiye da bukatar da Kano take da ita na su hada kansu domin su samarwa da Kano zaman lafiya da cigaba mai dorewa. 

A dalilin haka magoya bayansu sun dukufa wajen ganin jagoransu ne a sama ta kowane hali. Don haka cece-kuce ya kazanta a tsakanin juna. Da Allah zai sa idan aka kai karshen tirka-tirkar wadannan manyan biyu su yafewa juna su yi sulhu a tsakaninsu da zai fi kyau ga Kano da ma Kasa baki daya.

2. Karancin tazara tsakanin APC da NNPP ya sa kowa yana ganin ba zai ja da baya ga dayan ba. Wannan ce ta sa APC ba ta dangana ba game da zaben 2023 ta garzaya kotu. Sabanin abinda ya faru a zaben 2003, lokacin da Malam Ibrahim Shekarau ya karba daga hannun Injiniya Rabiu Musa Kwankwaso, wanda tazara tsakanin ANPP da PDP ta sa PDP ta saduda ba tare da ta je kotu ba. Haka ma a 2011, lokacin da Kwankwaso ya dawo ya karba daga hannun Shekarau. Ko da yake ANPP ta garzaya Kotu, amman shari’ar ba ta dauki hankali kamar a wannan karon ba, saboda sauran abubuwan da suka faru a wannan karon ba su faru a wancan lokacin ba. 

To amman fa karancin tazara a tsakanin jam’iyyu biyu bai kamata ya zama matsala ba. Hasali ma kamata ya yi ace ya zamo riba saboda jam’iyya mai mulki ta rika yin taka-tsantsan, sannan hamayyar siyasa ta sa a inganta shugabanci. Kuma idan an samu sauyi a zabe a dada samun ingancin shugabanci. Amman fa duk sai hamayyar da ake yi akan manufa ake yinta ta neman cigaban kasa da al’umma baki daya.

3. Yadda gwamnatin NNPP ta dauki wasu matakai a cikin garaje ya haifar da ta’azzara a hamayyar da ake yi a siyasar Kano. Alal misali, yadda aka kaddamar da bincike akan tsohon gwamna Ganduje nan take zai bashi hoton kamar ana son a ga bayansa ne a siyasance, don haka dole zai dauki matakai ba kawai na kare kansa ba amman har na ganin ya ga bayan abokan hamayyarsa a siyasance. Ya kamata ace an gane cewar idan Kwankwaso yana da gwamnatin Kano, Ganduje kuma yana tare da gwamnatin Tarayya. Da ace hada kansu suka yi wajen nemarwa Kano abinda zai amfaneta da ya fi su tsaya gwada kwanji. Akwai fatan bayan wannan dambarwas a samu daidaito a tsakanin shumagabannin biyu. Wani misalin shine yadda aka yi garaje wajen yin rusau daga hawan gwamnatin.
 Anan ba rusau dinne a karan kasa matsala ba. Amman rashin tsayawa a tantance, a kare wadanda ba su da hakki daga fadawa cikin hasarar da ba suji ba, ba su gani ba. Akwai fatan duk wani aiki da za a yi anan gaba a yi la’akari da kaucewa daukar hakki. Zai rage cece-kuce da fadawa cikin matsalar da za a iya kauce mata.

4. Karyewar kawancen siyasa tsakanin Shugaban Kasa, Bola Ahmad Tinubu, da Senator Rabiu Musa Kwankwaso ba za ta rasa nasaba da dagulewar harkokin siyasa a Kano ba. Da ace an yi wannan kawancen da hamayya za ta ragu tsakanin jagororin biyu, ko da ba ta kare gaba daya ba. Amman wannan karayar ta haifar da Karin masu hamayya da Senator Kwankwaso. 

Don haka siyasar ta Kano ta dada zafafa. Anan ‘yan Majalisar Tarayya na jam’iyyar NNPP suna da rawar da za su taka wajen samar da sasanci tsakanin Madugunsu da Shugaban Kasa. Yana da kyau su yi kokarin yin hakan. Su sun san hanyoyin da ake bi wajen yin hakan. Bukatar da Kano take da ita na neman zaman lafiya da karuwar arziki ita ya kamata a fifita.

5. Yakin ‘yan Media (Sojojin Baka) na bangarorin biyu ya ta’azzara hamayya a siyasar Kano. Yadda kowane bangare ya rika shiga kafafen yada labarai yana yanke hukunci akan shari’ar da ake yi ta zabe bai dace ba ko kadan. Yana da kyau a samu wasu su nemi Kotu ta haramta irin wannan dabi’ar a Shari’un da za a yi a nan gaba.

6. Kalaman tinziri da wasu jami’an gwamnati suka yi a gabanin yanke hukuncin shari’ar zaben na gwamnan Kano matsalace babba. Barazana ce ga tsarin shari’a da ma shugabanci baki daya. Wadanda suka yi wannan kalaman ba su yi la’akari da cewar gwamnatin jiha suke wakilta ba, kuma gwamnatin Taryya suke nunawa yatsa! Da sun yi la’akari da abinda yake samun ‘yan kungiyar IPOB, na yankin Igbo, da watakil ba su yi barazanar ba. Anan dole ne a yabawa gwamna Abba Kabir Yusuf game da matakin ladabtarwa da ya dauka nan take. Akwai bukatar duk mai kaunarsa ya kiyayi irin wannan kalaman daga nan har a gama appeal, da ma bayan an gama.

A karshe akwai bukatar ‘Yansiyasa su karanta dokar zabe ta Kasa, da ma sauran dokokin da suke da alaka da zabe, su yi kokari su fahimce su, su bisu sau da kafa. Wannan zai rage matsalolin zabe wadanda suke haifar da sai an kai ga shari’ar zabe. Haka kuma zai sa a fi fahimtar hukuncin da Kotunan zabe suke yankewa.

Muna fatan Allah Ta’ala ya tabbatar da zaman lafiya da karuwar arziki a Kano da Kasa baki daya.

Friday, 13 January 2023

Duk wanda ya yake ni Sai ya gane kurensa - Kwankwaso

Dan karar shugaban kasa na Jam’iar NNPP, Sana Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce duk wanda ya yake shi a Jihar Kano a zaben 2023, sai ya yaba wa aya zaki.

Jaridar Aminiya ta rawaito cewa Kalaman tsohon gwamnan jihar na zuwa ne bayan gwamna mai ci kuma wanda ba sa ga maciji, Abdullahi Ganduje, ya ce wa magoya bayan Jam’iyyar APC, a 2023 Kano za ta maimaita abin da ta yi a zaben shugaban kasa na shekarar 1993.


Ana ganin kalaman na Ganduje tamkar gugar zana ce cewa Kananawa ba za su zabi Kwankwaso ba a zaben da ke tafe a ranar 25 ga waan Fabrairu.

Amma a martanin Kwankwaso, ya ce, “Ba na son kula wancan mutumin, ban san ko ya fada ko bai fada ba, amma duk wanda ya yaki NNPP ko Kwankwaso a 2023 sai ya i da-na-sani.”


Ya ci gaba da cewa, “Duk wanda ya san ni, ya san abin da na yi a baya, ya san idan na ci zaben shugabna kasa, Kano za ta fi kowa amfana, Arewa za ta amfana, haka kuma kasa baki daya.”

A cewarsa, “Kwanan nan yi gangamin yakin neman zabe wadanda ke cikin mafiya kayatarwa, ba irin na wasu ’an takara da baki daga wasu jihohi suka shigo ba — Na yi daya a Wudil, Kudancin Kano, daya a Bichi, Arewacin Kano; sannan na bude ofishin yakin neman zabe a Kano ta tsakiya.

“Abin mamaki shi ne wai ni za a ce in kira gangamin yakin neman zabe a Kano; Sau nawa kuma; ko a kwananan daga watan Disamba zuwa Janairun nan na yi; don haka mene ne kaya gabas don ka yi akin neman zabe a Kano?”

Monday, 9 January 2023

2023: Dalilin Da Ya Sa Muka Tsayar Da Gawuna Takarar Gwamnan Kano– Ganduje

 


Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya ce masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a jihar sun tsayar da Mataimakinsa, Nasiru Yusuf Gawuna, a matsayin dan takarar Gwamnan jam’iyyar a zaben 2023 ne saboda kwarewarsa.

Ya ce biyayya da ilimi da kwarewa da kuma kyakkyawar mu’amalarsa da jama’a su ne suka karfafa zaben nasa.

Yana mai cewa, babu wata jam’iyya a Kano da ke da dan takara kwararre irin Gawuna.

Ganduje ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi a wajen taron gidauniyar da abokin Gawuna ya shirya a Abuja.

“Dokta Gawuna na sane da shirye-shirye da kuma ayyukanmu, kuma mun yi amannar mutum ne wanda zai taimaka wa cigaban al’uma.

“Wannan shi ne irin mutanen da muke raino, wadanda za su yi tsayin daka wajen ci gaba daga inda aka tsaya da kyawawan ayyukan bunkasa al’uma da aka asassa. Inshaa Allah za mu ci gaba da haka.

A cewar Ganduje, “Daya daga cikin abubuwan da muka yi la’akri da su shi ne ci gaba da ayyuka saboda muhimmancin hakan a sha’anin shugabannci.

“Mun tattara bayanan cigaban da muke bukata, kuma muddin aka rasa ci gaba wajen aiwatarwa abubuwa za su watse, ba za mu kai ko’ina ba.”

“Shi ya sa bayan ya tafi ban bukaci sai wani ya fada mini ayyukan da zan aiwatar ba saboda na san komai, kuma ba ni da dalilin yin watsi da su,” in ji shi.

A nasa bangaren, Gawuna ya ce ci gaba daga inda gwamnatin baya ta tsaya shi ne sirrin samun kyakkywan sakamako.

Ya kara da cewa, “Kwarewata na da muhimmanci, kuma a shirye nake in yi amfani da ilimin da na koya na shekaru wajen yi wa jiharmu hidima.”

(AMINIYA)

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...