Search This Blog

Showing posts with label Kujerun Hajji. Show all posts
Showing posts with label Kujerun Hajji. Show all posts

Monday, 1 May 2023

Duk da tsadar aikin Hajjin bana, kujeru 3,132 na Bauchi sun ƙare har ana nema

 


Kujerun aikin hajji 3,132 da Hukumar Alhazai ta
Ƙasa, NAHCON ta baiwa jihar Bauchi sun ƙare ƙarƙaf, duk da tsadar kudin aikin hajjin na bana da ya kai N2,919,000.

Babban Sakataren Hukumar Alhazai ta Bauchi, Imam Abdurrahman Ibrahim Idris ne ya bayyana haka a wani shiri na addini da rayuwa na gidan talabijin na NTA Bauchi, wanda ya gudana jiya Asabar 29 ga Afrilu, 2023.

A wata sanarwa da Muhammad Sani Yunusa Jami’in Yada Labarai na hukumar ya fitar a yau Lahadi, ya ce shirin talbijin din wani yunkuri ne na hukumar don sanar da al’umma halin da ake ciki kan shirye-shiryen aikin Hajjin 2023.

Imam Abdurrahman ya ce “Ba mu da sauran gurbi na kujerun aikin hajji, amma mun mika bukatar ga hukumar alhazai ta kasa don neman kari wa maniyyatan mu”.

Ya alakanta tashin farashin hajjin bana da tsadar masaukai a kasar Saudiyya da kuma faduwar darajar Naira akan Dalar Amurka.

Da ya taɓo batun bita, Imam Abdurrahman ya ce ba a yin ibada cikin jahilci, inda ya kara da cewa neman ilimi ga musulmi don bashi damar gudanar da ayyukansa na ibada yadda ya kamata ya zama tilas.              

Ya roki malaman bita a cibiyoyin bita da ke fadin jihar da su tallafawa maniyyata yadda ya kamata, inda ya kuma ja hankalin maniyyatan da su yi anfani da damarsu don sanin hukunce+hukuncen aikin Hajji.

Ya yi amfani da kafar sadarwar wajen nanata kudurin Gwamna Bala Abdulkadir Muhammad na ganin jihar Bauchi ta ci gaba da rike sunanta a matsayin Wanda tayi fice wajen tallafawa alhazai.

DN

Saturday, 4 February 2023

Hajj2023: Hukumar NAHCON Ta Bawa Kano Kujerun Hajji 2,902

Rabon ya kasance kamar haka:

Abia 53

Adamawa. 2669

Anambara. 39

Bauchi. 3, 132

Bayelsa. 35

Binuwai. 236

Borno. 2,735

Cross Rivers. 66

Delta 74

Nassarawa. 1,567

Nijar. 5,165

Ogun. 1,139

Ondo 436

Osun. 1,054

Oyo. 1 441

Yobe. 1,968

Ebony 117

Edo 274

Ekiti. 197

Enugu. 40

FCT 3,520

 

 

Gombe. 2,301

Imo. 30

Jigawa. 1,525

Kaduna. 5982

Kano. 5,902

Katsina. 4,913

 

Kebbi. 4871

Kwara. 3,219

Legas. 3,576

Plateau. 1,984

Rivers. 50

Sokoto. 5,504

Taraba. 1,590

Za a saki jihar Kogi ne bayan kammala nazarin ayyukanta yayin da aka dakatar da rabon jihar Akwa Ibom saboda rashin sabunta lasisin aiki.

A halin da ake ciki, ana sa ran dukkan jihohin za su mika wa Hukumar biyan kashi 50% na kudin kujerun 2022 kafin ranar 10 ga watan Fabrairu. 

Rashin yin hakan ka iya sanyawa a rage yawan adadin kujerun da aka bawa jahar 
 

 

HANNU

Mousa Ubandawaki

Mataimakin Daraktan Labarai da wallafe-wallafe

NAHCON, Abuja

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...