Posts

Showing posts with the label Gangami

Ma'aikatar Ilimi Ta Kano Ta Fara Gangamin Wayar Da Kai Kan Shirin Gwamnati Na Ayyana Dokar Tabaci Kan Ilimi.

Image
  Yayin Da Tawagar Takai Ziyarar Karaye Da Masarautar Rano A shirye-shiryen ayyana dokar ta-baci kan ilimi a hukumance da gwamnatin Alhaji Abba Kabir Yusuf, ma'aikatar ilimi ta jihar Kano ta fara gangamin wayar da kan jama'a kan sabbin manufofin ilimi. A sanarwar da daraktan wayar kan jama'a na ma'aikatar, Balarabe Abdullahi Kiru ya sanyawa hannu, yace wata tawaga mai karfi a karkashin jagorancin kwamishinan ilimi na jihar a yau ta ziyarci masarautun Karaye da Rano domin wayar da kan al’ummar yankunan kan shirin gwamnati na ayyana dokar ta-baci kan ilimi. Da yake jawabi a fadar Mai Martaba Sarkin Karaye Dr. Ibrahim Abubakar II, Kwamishinan Ilimi na Jihar Alhaji Umar Haruna Doguwa ya bayyana cewa a ranar 6 ga Mayu, 2024 gwamnatin jihar Kano za ta kafa dokar ta-baci a fannin ilimi. Kwamishinan ya bayyana cewa da wannan sanarwar, ilimi zai kasance kan gaba, domin bangaren farko da ke samun fifikon gwamnati shi ne ginshikin ci gaban dan Adam. A karkashin wannan