Posts

Showing posts with the label Kayan abinci

Ramadan: Gwamna Yusuf ya bada tallafin kayan abinci ga ma'aikatan gidan gwamnati

Image
Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bayar da tallafin kayan abinci na miliyoyin Naira ga ma’aikatan gidan gwamnatin da ke aiki tare a wani bangare na mika musu na watan Ramadan. Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar a ranar Lahadi. Sanarwar ta ce nau'ikan kayan da aka rabawa  masu matakin albashi na 1 zuwa na 12 sun hada da buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 50, da katon macaroni, laka na gero guda goma, da kuma kudi N10,000 kowanne. Da yake gabatar da kayayyakin cikin yanayi na musamman, gwamnan ya bayyana godiyarsa ga Allah da ya ba shi damar yin hakan da nufin ganin an samu nasara ga ma’aikatan sa a cikin watan Ramadan mai albarka. “Yau rana ce ta musamman ba a gare ni kadai ba har ma’aikata na a gidan gwamnati domin na fara cika alkawuran yakin neman zabe na na inganta ayyukan jin dadi ga ma’aikatan gwamnati.” Ya bayyana. Gwamnan ya ci gaba da bayyana cewa za a ci

Jam’ar Gari Sun Wawushe Kayan Abincin Da Gwamnati Ta Killace

Image
  Jama’ar gari sun wawushe kayan abinci da gwamnati ta killace a wanin rumbun ajiyarta tun a shekarar 2022 da nufin za ta raba domin rage radadin ibtila’in ambaliyar ruwa.  Mutanen sun yi kukan kura ne suka fasa rumbun ajiyar hatsi da sauran kayan abincin Gwamnatin Jihar Bayelsa, suka kwashen kayan abincin da suka samu a ciki. Sai dai Hukumar Agajin Gaggawa ta jihar (SEMA) ta sanar cewa kayayyakin abincin da aka kwashe sun riga sun lalace, kuma duk wanda ya ci zai samu matsala. Babban daraktan hukumar, Walamam Sam Igrubia, ya ce a shirinsu na tunkarar ambaliyar ruwa a bana, shugaban hukumar ya ziyarci wurin, inda ya iske kayan abincin da suka rage, musamman shinkafa da garin rogo ba za su ciwu ba. Wannan dai shi ne karo na biyu, bayan an Jihar Adamawa inda jama’a ke fasawa su kwashe yakan abinci daga rumbunan ajiyar kayan abinci, sakamakon tsananin tsadar kayan masarufi da ’yan Najeriya ke fama da shi. Tun bayan cire tallafin man fetur a kasar farashinsa ke ta ninkuwa, wanda hakan ya h