Search This Blog

Showing posts with label Zaben Shugaban Kasa. Show all posts
Showing posts with label Zaben Shugaban Kasa. Show all posts

Monday, 15 May 2023

Al'ummar Turkiya za su kada kuri'a a zagaye na 2 na zaben shugaban kasa

 


karon farko al’ummar Turkiya na shirin kada kuri’a a zagaye na biyu na zaben shugaban kasa, bayan koma bayan da shugaba Recep Tayyib Erdogan ya samu da ya hana shi iya lashe zagaye na farko na zaben duk kuwa da tazarar yawan kuri’u.

Shugaba Recep Tayyib Erdogan da ke jagorancin Turkiyya tun daga shekarar 2003, wannan ne karon farko da sakamakon zabe ke nuna ya gaza samun kasha 50 na yawan kuri’un da aka kada duk da cewa akwai gagarumar rata tsakaninsa da babban abokin karawarsa.

Gabanin fitar sakamakon zaben, shugaba Recep Tayyib Erdogan yayin jawabi gaban dandazon magoya baya, ya bayyana cikakken shirin da ya ke dashi na sake jan ragamar Turkiya zuwa shekaru 5 a nan gaba.

Shugaba Recep Tayyib Erdogan.
Shugaba Recep Tayyib Erdogan. via REUTERS - MURAT CETINMUHURDAR/PPO

Erdogan mai shekaru 69 ya yi ikirarin cewa jam’iyyarsa mai rajin bin tafarkin addinin Islama ta lashe galibin kujerun Majalisa, sai dai alkaluman da kamfanin dillancin labaran kasar ya wallafa sun nuna Erdogan a matsayin wanda ya lashe kashi 49.3 yayinda jagoran adawa Kemal Kilicdaroglu ke da kashi 45.

Wannan sakamako gad an adawa Kemal dai babban koma baya ne lura da yadda kuri’ar jin ra’ayin jama’a gabanin zabe a baya ta nuna shi a matsayin mai rinjaye.

Yanzu haka dai dukkanin bangarorin biyu za su zage damtse don tunkarar zagaye na biyu da aka tsara zai gudana ranar 28 ga watan da muke na Mayu.

RFI

Tuesday, 14 March 2023

‘Kusan Sau Miliyan 13 Aka Yi Yunkurin Yi Wa Najeriya Kutse Yayin Zaben Shugaban Kasa’


 Gwamnatin Tarayya ta ce akalla sau 12,988,978 aka yi yunkurin yin kutse a shafukan intanet na Najeriya yayin zaben Shugaban Kasa da na ’yan Majalisun Tarayya da aka yi a ranar 25 ga watan da ya gabata.

Hare-haren, a cewar gwamnatin an kai su ne daga ciki da wajen kasar, kuma an yi su ne kan shafukan gwamnati, kusan sau 1,550,000 a kullum.

Ministan Sadarwa, Isah Ali Pantami ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa ranar Talata.

To sai dai ya ce yunkurin kutsen ya yi tashin gwauron zabo zuwa sau 6,997,277, a ranar zaben Shugaban Kasa ta Asabar.

Ministan ya kuma ce ma’aikatarsa ta kafa wani kwamitin yaki da irin wadannan hare-haren, kuma ya fara aiki ne ranar 24 ga watan na Fabrairu, sannan ya kammala ranar 28.

AMINIYA

Thursday, 2 March 2023

Zamu Kalubalanci Zaben Shugaban Kasa - Atiku Abubakar

Ɗan takarar shugaban ƙasa na babbar jam’iyyar hamayya a Najeriya, PDP, Atiku Abubakar ya ce dole ne kowa ya ƙalubalanci zaɓen da aka yi na ranar 25 ga watan Fabarairu.

A taron manema labarai da ya gabatar a Abuja, tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya ce, abin da ya faru a kan zaɓen fyaɗe ne aka yi wa dumukuradiyya.

Atiku ya ce, a tarihin ƙasar wannan shi ne zaɓe mafi muni da aka taɓa yi, wanda kuma dama ce ta sake daidaita Najeriya.

Amma kuma hukumar zaɓen ƙasar, INEC ta lalata tare da watsa wannan dama da buri na ‘yan Najeriya.

Ɗan takarar na PDP, ya ce zaɓen ya kasa kaiwa matsayi da matakin da aka sa rai zai kai.

Sannan ya ce lauyoyinsu suna duba lamarin kafin su san matakin da za su ɗauka na gaba.

Ya ce idan har ya je kotu ba a yi masa adalci ba to zai bar su da Allah.

Za mu kawo muku karin bayani a nan gaba.
BBC 

Tuesday, 28 February 2023

Labari da dumiduminsa : INEC Ta Bayyana Bola Tinubu A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Shugaban Kasa

An ayyana Bola Tinubu, dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC), a matsayin wanda ya lashe zaben shugaban kasa.

Shugaban Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC), Mahmood Yakubu ne ya sanar da sakamakon zaben a safiyar yau Laraba.


Yakubu ya ce Tinubu ya samu kuri’u 8,794,726.


Atiku Abubakar na jam’iyyar PDP ne ya samu kuri’u 6,984,520, yayin da Peter Obi na jam’iyyar Labour Party (LP) ya zo na biyu da kuri’u 6,101,533.

"Yanzu na sauke nauyin da ya rataya a wuyana a matsayina na babban jami'in dawo da na kasa," in ji shugaban INEC.


“Ni, Farfesa Mahmood Yakubu, a nan na tabbatar da cewa ni ne jami’in da zai dawo takara a zaben 2023. An fafata zaben.

“Wannan Tinubu Bola Ahmed na jam’iyyar APC, bayan ya tabbatar da ka’idojin doka, an bayyana shi a matsayin wanda ya yi nasara kuma an dawo da shi.

Yakubu ya kara da cewa za a bayar da takardar shaidar komawa ga Tinubu da karfe 3 na yammacin Laraba.

Thursday, 23 February 2023

Yau Ake Rufe Yakin Neman Zaben Shugaban Kasa

 


Daga karfe 12 na daren yau Alhamis 23 ga Fabrairu, 2023, za a fure yakin neman zaben ’yan takarar shugaban kasa da Majalisun Tarayya da za a gudanar ranar Asabar.

Dokar Zaben Najeriya ta haramta yin duk wani nau’in yakin neman zabe ko tallata dan takara daga sa’a 24 kafin ranar zabe.

A yayin rubuta wannan rahoton, kusan awa 12 ya rage wa daukacin jam’iyyu da ’yan takara su yi duk abin da za su iya, su kuma rufe yakin neman zabensu, sannan a fafata a akwatunan zabe a ranar Asabar.

Jam’iyyu 18 ne ke zawarcin kujerar shugaban kasa bayan kammala wa’adin Shugaba Muhammadu Buhari na biyu a ranar 29 ga watan Mayu.

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta bayyana cewa za a gudanar da zabukan ne a mazabu 1,491 da ke kananan hukumomi 774 da ke jimillar rumufunan zabe 176, 846.

’Yan Najeriya ne za su yi alkalanci a zaben mai mutum miliyan 95.5 da suka yanki katin zabe, wadanda akasarinsu matasa ne, masu shekara 18 zuwa 35, ko da yake kawo yanzu babu alkaluman adadin wadanda suka karbi katin zabensu.

Manyan jam’iyyu

Jam’iyyar APC mai mulki kasar tun 2015 na neman ci gaba da jan ragamar kasar na karin shekara hudu, a yayin da babbar jam’iyyar adawa ta PDP wadda ta mulki kasar na tsawon shekara 16, bayan dawowar tsarin dimokuradiyya daga 1999 zuwa 2015 na neman sake dawowa.

Bugu da kari, zaben na bana ya zo da sabon abu, inda ake da wasu kananan jam’iyyu biyu, LP da kuma NNPP da suke tashe da kuma samun magoya baya a wannan karon.

Batun shekarun ’yan takara dai ya dade yana tayar da kura a zabukan Najeriya, inda gabanin zaben 2019 Gwamnatin Tarayya ta yi dokar rage yawan shekarun tsayawa takara domin a dama da matasan kasa.

APC ta tsayar da tsohon Gwamnan Jihar Legas (1999-2007) kuma Uban Jam’iyyar na kasa, Asiwaju Bol Ahmed Tinubu, a yayin da PDP ta tsayar da Fsohon Mataimkin Shugaban Kasa Atiku Abubakar (1999-2007).

Karo na biyar ke nan Atiku yake neman zama shugaban kasa a yayin da Tinubu ke tutiyar cewa shi ya fi kowa dacewa ya mulki kasar a wannan karon bayan Buhari.

A nasa bangaren, yana takama da matasa, kasancewarsa mai karancin shekaru a cikin manyan ’yan takara.

Hakazalika, dan takarar NNPP, Sanata Rabiu Musa Kwankwaso yana takama da kasancewa mai jini a jika yana kuma bugun gaba da irin ayyukan da ya yi a lokacin da yake Gwamnan Jihar Kano, ministan tsaro.

Yana kuma takama da farin jininsa, inda a 2015 ya zama na biyu a zaben dan takarar shugaban kasa na APC, wanda Buhari ya lashe.

Zaben na zuwa ne a yayin da Najeriya ke tsaka da fama da matsalar tattalin arziki bayan Gwamnatin APC ta yi sauyin takardun Naira 200, N500 da kuma N1,000.

Sauran abubuwan da ke ci wa kasar tuwo a kwarya sun hada da sha’anin tsaro, tsadar man fetur da rashin ingantattun ababen more rayuwa da suka hada da bangaren ilimi, lafiya, sufuri, da kuma uwa uba makamshi da wutar lantarki.

Tuesday, 17 January 2023

A shirye muke don zuwa zagaye na biyu a zaɓen shugaban ƙasa - Shugaban INEC

Shugaban Hukumar Zaɓe mai zaman ƙanta a Najeriya Farfesa Mahmood Yakubu ya ce hukumarsa a shirye take game da zuwa zaɓen zagaye na biyu na shugaban ƙasar idan har ba a samu wanda ya yi nasara a zagayen farko ba.

Farfesa Yakubu ya bayyana hakan ne a lokacin da yake jawabi kan shirye-shiryen hukumar na tunkarar babban zaɓen ƙasar da ke tafe a Chatham House da ke birnin Landan a Birtaniya.

Ya ƙara da cewa a INEC ta yi shirin yiyuwar zuwa zagaye na biyu a zaɓen shugaban ƙasar, kamar yadda take yi a zaɓuka uku da suka gabata.

Shugaban hukumar zaɓe ya kuma ce zaɓen ƙasar da za gudanar cikin wannan shekara zaɓe ne na matasan ƙasar.

Farfesa Yakubu ya kuma ce rajistar masu kaɗa ƙuri'a ta nuna cewa matasa ne suka mamaye adadi mafi yawa na masu rajistar zaɓen.

Shugaban Hukumar ya ce ya ji daɗin yadda mutane suka fito domin karɓar katinan zaɓensu, yana mai cewa fiye da mutum 600,000 sun karɓi katinansu a jihar Legas kaɗai cikin watan da ya gabata.

Ya ƙara da cewa a yanzu adadin masu rajistar zaɓe a Najeriya sun kai miliyan 93.4, kuma daga ciki miliyan 37 wato kashi 39 na rajistar zaɓen matasa ne 'yan tsakanin shekara 19 zuwa 34.

Ya kuma tunasar da maharta taron cewa hukumar za ta tsayar da rabar da katin zaɓen daga ranar 29 ga watan Janairun da muke ciki.
(BBC HAUSA) 


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...