Search This Blog

Friday, 6 January 2023

An haramta cire tsabar kudi daga asusun Gwamnati

Hukumar da ke sanya ido kan hada-hadar kudade a Najeriya (NFIU) ta haramta cire tsabar kudi daga asusun Gwamnatin Tarayya da jihohi da kuma kananan hukumomi daga ranar 1 ga watan Maris, 2023.

NFIU ta ce daga ranar, laifi ne a biyan ma’aikatan gwamnati alawus-alawus din tafiyar aiki a cikin gida ko zuwa kasashen waje da tsabar kudi.

An gano gawar mutum 16 a hatsarin jirgi a Kebbi
’Yan sanda sun cafke ’yan daba 63 a taron Tinubu a Kano
Babban Daraktan hukumar, Modibbo Tukur, ne ya bayyana haka a Abuja ranar alhamis, inda ya ce karin wasu sabbin tsare-tsaren na tafe.

Ya ce za a fara amfani da sabbin tsare-tsaren ne bayan fara aikinsa dokar Babban Bankin Najeriya (CBN) na takaita cirar tsabar kudi ga daidaikun mutane da kamfanoni a Najeriya.


Da yake karin haske kan dokokin, Modibbo ya ce hakan yayi daidai da sashi na 3(1)a-s, da sashi na 23(2) na kundin hukumar.

A baya dai bisa dalilai daban-daban, ma’aikatun gwamnati da hukumomi, na fitar da kudade daga bankuna don yin mu’amalar kasuwanci a hukumance da ba a iya ganowa cikin sauki, maimakon ta hanyar musayar bankuna.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Head of Service Urges Civil Servants to Uphold Ethical Conduct

The Head of Service, Kano State, has called on civil servants to strictly adhere to the Civil Service ethical code and show grea...