Search This Blog

Showing posts with label 'Yan Najeriya. Show all posts
Showing posts with label 'Yan Najeriya. Show all posts

Friday, 2 June 2023

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Bai Wa ’Yan Najeriya Tallafi

 


Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya ba da umarnin bayar da tallafi domin rage wa ’yan Najeriya domin rage musu radadin cire tallafin mai da Gwamnatin Tarayya ta yi.

Shugaban Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) Mele Kyari ne ya sanar da haka, yana mai cewa biyan tallafin mai da gwamnati ke yi ya zama tarihi, hasali ma ba a ware masa ko sisi ba a kasafin kudi.

Da yake bayani bayan ganawarsa da jagororin jam’iyyar APC mai mulki, Kyari ya ce a halin yanzu ma NNPC na bin gwamnati bashin Naira tiriliyan 2.8 da ya kashe wajen biyan tallafin man, don haka kamfanin ba zai iya ci gaba da biya ba.

“Har yanzu gwamnati ta kasa biyan Naira 2.8 da muke bin ta, wanda ya isa hujja cewa gwamnati ba za ta iya ci gaba da biyan tallafin man ba,” in ji Kyari.

Ya bayyana cewa babu wanda zai ba da bashi ga wanda ake bi bashin Naira tiriliyyan 2.8, don haka, kamfanin NNPCL ba zai iya kara biyan tallafin a madadin gwamnati ba.

Hasali ma kudin da NNPC ke kashewa wajen biyan tallafin na hana shi sauke nauyin da ya rataya a kansa, ga shi kasa na bukatar kudaden aiwatar da manyan ayyuka da samar da ababen more rayuwa.

A gefe guda kuma, kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International ta yi kira ga gwamnatin Najeriya da ta dauki matakan da za su hana cire tallafin man jefa ’yan kasar cikin karin matsin rayuwa.

Mukaddashin daraktan Amnesty International, Isa Sanusi, ya shawarci gwamnati ta yi hattara kada matakin nata ya kara talauta ’yan kasar “wadanda da kyar suke iya biyan kudin makaranta da na asibiti da kuma cefani.

“Ga shi kuma har yanzu gwamnatin ba ta fayyyace matakan da za ta dauka domin rage radadin cire tallafin a kan masu karamin karfi ba.

“Bai kamata cire tallafin ya kara kawo kuncin rayuwa ga jama’a ba, don haka akwai bukatar daukar matakai da za su samar da sauki bayan janye tallafin man.

“Bai dace Najeriya ta ci gaba da biyan tallafin da aka dade ana wuru-wuru da shi ba, kuma ya kamata gwamnati ta amsa kiraye-kirayen hukunta duk wadanda aka samu da laifi a badakalar tallafin mai a rahoton da majalisar dokoki ta gudanar — komai matsayin wanda aka kama da laifin.

AMINIYA

Thursday, 27 April 2023

Saudiyya Ta Kwashe ’Yan Najeriya Da Suka Makale A Sudan Zuwa Kasarta


Gwamnatin kasar Saudiyya ta kwashe wasu daga cikin ’yan Najeriya da suka makale a yakin da ya barke a Sudan zuwa kasarta.

Minista a Ma’aikatar Harkokin Waje ta Najeriya, Zubairu Dada, ya ce Saudiyya ta tura jiragen ruwa da suka kwashe ’yan Najeriya zuwa birnin Jeddah na kasarta, bayan barkewar yaki a Sudan.

Ma’aikatar ta ce daga bisani za a maido da ’yan Najeriyan da aka kai Saudiyya gida, kuma gwamnatin Tarayya na kokarin ganin cewa babu dan Najeriya ko daya da ya rage a Sudan kafin cikar wa’adin awa 72 da bangarorin da ke yaki da juna suka bayar na tsagaita wuta.

Ta bayyana cewa a kokarinta na kwashe ’yan Najeriya da suka makale bayan barkewar yakin, Gwamnatin Tarayya ta kashe Naira miliya 552 kan daukar hayar motocin da za su fitar da su zuwa iyakar Sudan da kasar Masar.

Ministan Harkokin Waje na Najeriya, Geoffrey Onyema, ya ce an dauki hayar bas-bas 40 da za su kwashi ’yan Najeriya daga Khartoum, babban birnin Sudan zuwa iyakar kasar Masar da ke Aswan, inda za su hau jirgi zuwa gida.

“Dala miliyan 1.2 (Naira miliyan 552) aka caje mu kan bas 40 da muka nema; Mun samu bas guda 40 na alfarma da za su dauki ’yan Najeriya (daga Khartoum) zuwa iyakar kasar Masar.

“Sanin kowa ne cewa tabbas irin wannan yanayi akwai wadanda za su yi amfnai da rikicin Sudan wajen tatsar jama’a,” in ji Oyema.

Ya bayyana cewa Gwamnatin Tarayya na yin dukkan mai yiwuwa wajen ganin an gama kwashe ’yan Najeriya cikin sa’a 72 da gwamnatin Sudan ta bayar na tsagaita wuta.

“Ba mu da matsala da wa’adain awa 72 da gwamnatin ta bayar kuma mun tattauna da bangarorin da abin ya shafa, kuma sun ba mu hadin kai,” in ji shi.

Ya ci gaba da cewa “Za a kwashe ’yan Najeriya ne a rukuni-rukuni domin tabbatar da tsaron lafiyarsu; kuma Alhamdulillah babu dan Najeriya ko daya da ya rasa ransa.

AMINIYA

Monday, 30 January 2023

Buhari ya yi kira ga 'yan Najeriya su riƙa gode wa Allah

 


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce abubuwan more rayuwa da ake ginawa a faɗin ƙasar 'abin ban sha'awa' ne.

A wata sanarwa mai mai magana da yawun shugaban ƙasar Femi Adesina ya fitar, Shugaba Buhari ya yi kira ga 'yan ƙasar da su riƙa yaba wa da abubuwan more rayuwa da ake gina musu, la'akari da yanayin da ƙasar ke ciki idan an kwatanta da sauran ƙasashe.

Shugaban na jawabi ne a lokacin da yake kammala ziyarar aiki ta yini guda da ya kai jihar Kano da ke arewacin ƙasar domin ƙaddamar da wasu ayyukan da gwamnatin jihar da ta tarayya da kuma wasu kamfanoni masu zaman kansu suka yi.

Shugaban ya ce ‘‘muna da ƙasaitacciyar ƙasa, amma ba ma yaba mata, har sai mun ziyarci ƙasashe maƙwabta da sauran ƙasashe, inda sai mutane sun yi da gaske sannan su sami abinci sau ɗaya a rana''.

‘‘A lokacin da nake shawagi a cikin jirgi adadin dogayen gine-ginen da na gani da yawan ci gaban da ake da shi a doron ƙasa abin ' ban sha'awa' ne. Mun gode wa Allah, Mun gode wa Allah'', in ji Buhari.

Shugaban ƙasar ya kuma umarci manyan 'yan ƙasar da su ƙarfafa wa matasa gwiwwa wajen rungumar ilimi, yana mai cewa dole ko ana so, ko ba a so makomar ƙasar a hannun matasan take.

Ya ce '‘dole su rungumi ilimi, Fasaha ta saukaka abubuwa da dama, to amma babu abin da zai maye gurbin ilimi, dan Allah ku ƙarfafa wa yara gwiwwa su samu ilimi''.

Shugaban ya kuma jinjina wa gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje bisa ayyukan raya jihar da ya shimfiɗa, yana mai cewa a ziyarar baya-bayan nan da ya kai jihohin Kogi da Yobe da Legas da Katsina ya nuna cewa, gwamnonin waɗannan jihohi sun yi namijin ƙoƙari, wajen yin ayyukan raya ƙasa a jihohin nasu idan aka kwatanta da kuɗaden da suke samu.

(BBC)

Tuesday, 10 January 2023

Na Cika Alkawuran Da Na Daukar Wa ’Yan Najeriya – Buhari

Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, ya ce ya cika alkawuran da ya dauka na yaki da ’yan ta’addan boko Haram da farfado da tattalin arziki da kuma yaki da cin hanci da rashawa.

A cewar Kakakin Shugaban, Femi Adesina, Buhari ya bayyana hakan ne yayin wanin taron cin abinci da aka shirya domin karrama shi a Damaturu, babban birnin jihar Yobe.

Giwa ta kashe manomi a Uganda
’Yan bindiga sun harbe jami’an tsaro 12 a Kaduna
Shugaban dai ya fara ziyarar yinin biyu ne a Jihar ranar Litinin.

Sanarwar ta kuma ce Shugaban ya bigi kirjin cewa babu wanda zai zarge shi da tara dukiyar da ba ta halas ba lokacin da yake mulki, inda ya ce ko taku daya ba shi da shi a wajen Najeriya.
A wani labarin kuma, Shugaban ya ce babu wata kungiyar ’yan ta’adda da ta isa ta wargaza Najeriya.

Shugaban Kasar ya bayyana haka ne yayin da ya kai ziyara fadar Sarkin Damaturu, Alhaji Hashumi Ibn Elkanemi II a fadarsa da ke garin Damaturu, ranar Talata.

Buhari ya kuma bukaci ’yan Najeriya da su kara kaimi tare da ba da karfin gwiwa ga hukumomin tsaro kan kokarinsu na zaman Najeriya kasa daya dunkulalliya.

“A watanni hudu masu zuwa, in na bar mukamin Shugaban Kasa, zan ci gaba ne da dagewa, kuma ina fatan zan aiki lafiya.”

“Dole ne mu samar da kwarin gwiwa a kasarmu tare da tabbatar da cewa ba mu kawo cikas ga tsaro ba ta kowace fuska domin tsaro da tattalin arziki su ne mafi muhimmanci ga kowace kasa.

“Mun sha fama da yawa wajen hada kan kasar nan, kuma ina rokon ku da ku dage da tabbatar da cewa ba za mu bari wani ya sake wargaza mu ba,” in ji shi.

Shugaban ya kuma bayyana farin cikinsa da dawowar zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Yobe da ma yankin Arewa maso Gabashin Najeriya, inda ya gode wa Gwamnan Yobe, Mai Mala Buni da takwaransa na jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, bisa jajircewar da suka yi na sake gina makarantu, cibiyoyin lafiya da cibiyoyin da ’yan ta’addan suka lalata.

Shugaban ya ce, ya lura da cewa ‘’da gangan aka yi yunkurin ruguza Najeriya amma Allah bai yarda ba,’’ ya kara da cewa ‘’Allah ya taimaki Najeriya ta dawo.

Ya kuma yabawa jami’an soji da ‘yan sanda bisa sadaukarwar da suke yi wajen kare Kasar nan daga fadawa cikin mummuna yanayi.

Shugaban ya kara da cewa, da suka yi yaki don kare hadin kan Najeriya a lokacin yakin basasa, wadanda ke cikin wannan kwarewa ba za su taba barin wani ya sake ruguza kasar nan ba

Da ya ke jawabi, Gwamna Buni ya shaida wa Shugaban Kasar cewa, a cikin wannan yakin da ake yi da ’yan tada kayar baya, ’yan ta’adda sun taba mamaye hatta fadar Sarkin Damaturu a baya.

Sai dai ya ce tun bayan zuwan gwamnatin APC a 2015, Jihar ta samu sa’ida.

Shi kuwa Sarkin na Damaturu ya mika godiyarsa ga Shugaban Kasar kan inganta harkokin tsaro a kasar, inda ya ce, “Mun sha wahala a baya, amma gwamnatinka ta hada kan kasa cikin ikon Allah.”
(AMINIYA) 

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...