Posts

Showing posts with the label 'Yan Najeriya

Tinubu Ya Ba Da Umarnin Bai Wa ’Yan Najeriya Tallafi

Image
  Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu ya ba da umarnin bayar da tallafi domin rage wa ’yan Najeriya domin rage musu radadin cire tallafin mai da Gwamnatin Tarayya ta yi. Shugaban Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) Mele Kyari ne ya sanar da haka, yana mai cewa biyan tallafin mai da gwamnati ke yi ya zama tarihi, hasali ma ba a ware masa ko sisi ba a kasafin kudi. Da yake bayani bayan ganawarsa da jagororin jam’iyyar APC mai mulki, Kyari ya ce a halin yanzu ma NNPC na bin gwamnati bashin Naira tiriliyan 2.8 da ya kashe wajen biyan tallafin man, don haka kamfanin ba zai iya ci gaba da biya ba. “Har yanzu gwamnati ta kasa biyan Naira 2.8 da muke bin ta, wanda ya isa hujja cewa gwamnati ba za ta iya ci gaba da biyan tallafin man ba,” in ji Kyari. Ya bayyana cewa babu wanda zai ba da bashi ga wanda ake bi bashin Naira tiriliyyan 2.8, don haka, kamfanin NNPCL ba zai iya kara biyan tallafin a madadin gwamnati ba. Hasali ma kudin da NNPC ke kashewa wajen biyan tallafin na hana shi sauke nauyin da ya rata

Saudiyya Ta Kwashe ’Yan Najeriya Da Suka Makale A Sudan Zuwa Kasarta

Image
Gwamnatin kasar Saudiyya ta kwashe wasu daga cikin ’yan Najeriya da suka makale a yakin da ya barke a Sudan zuwa kasarta. Minista a Ma’aikatar Harkokin Waje ta Najeriya, Zubairu Dada, ya ce Saudiyya ta tura jiragen ruwa da suka kwashe ’yan Najeriya zuwa birnin Jeddah na kasarta, bayan barkewar yaki a Sudan. Ma’aikatar ta ce daga bisani za a maido da ’yan Najeriyan da aka kai Saudiyya gida, kuma gwamnatin Tarayya na kokarin ganin cewa babu dan Najeriya ko daya da ya rage a Sudan kafin cikar wa’adin awa 72 da bangarorin da ke yaki da juna suka bayar na tsagaita wuta. Ta bayyana cewa a kokarinta na kwashe ’yan Najeriya da suka makale bayan barkewar yakin, Gwamnatin Tarayya ta kashe Naira miliya 552 kan daukar hayar motocin da za su fitar da su zuwa iyakar Sudan da kasar Masar. Ministan Harkokin Waje na Najeriya, Geoffrey Onyema, ya ce an dauki hayar bas-bas 40 da za su kwashi ’yan Najeriya daga Khartoum, babban birnin Sudan zuwa iyakar kasar Masar da ke Aswan, inda za su hau jirgi zuwa gi

Buhari ya yi kira ga 'yan Najeriya su riƙa gode wa Allah

Image
  Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce abubuwan more rayuwa da ake ginawa a faɗin ƙasar 'abin ban sha'awa' ne. A wata sanarwa mai mai magana da yawun shugaban ƙasar Femi Adesina ya fitar, Shugaba Buhari ya yi kira ga 'yan ƙasar da su riƙa yaba wa da abubuwan more rayuwa da ake gina musu, la'akari da yanayin da ƙasar ke ciki idan an kwatanta da sauran ƙasashe. Shugaban na jawabi ne a lokacin da yake kammala ziyarar aiki ta yini guda da ya kai jihar Kano da ke arewacin ƙasar domin ƙaddamar da wasu ayyukan da gwamnatin jihar da ta tarayya da kuma wasu kamfanoni masu zaman kansu suka yi. Shugaban ya ce ‘‘muna da ƙasaitacciyar ƙasa, amma ba ma yaba mata, har sai mun ziyarci ƙasashe maƙwabta da sauran ƙasashe, inda sai mutane sun yi da gaske sannan su sami abinci sau ɗaya a rana''. ‘‘A lokacin da nake shawagi a cikin jirgi adadin dogayen gine-ginen da na gani da yawan ci gaban da ake da shi a doron ƙasa abin ' ban sha'awa' ne. Mun gode wa Allah, Mu

Na Cika Alkawuran Da Na Daukar Wa ’Yan Najeriya – Buhari

Image
Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, ya ce ya cika alkawuran da ya dauka na yaki da ’yan ta’addan boko Haram da farfado da tattalin arziki da kuma yaki da cin hanci da rashawa. A cewar Kakakin Shugaban, Femi Adesina, Buhari ya bayyana hakan ne yayin wanin taron cin abinci da aka shirya domin karrama shi a Damaturu, babban birnin jihar Yobe. Giwa ta kashe manomi a Uganda ’Yan bindiga sun harbe jami’an tsaro 12 a Kaduna Shugaban dai ya fara ziyarar yinin biyu ne a Jihar ranar Litinin. Sanarwar ta kuma ce Shugaban ya bigi kirjin cewa babu wanda zai zarge shi da tara dukiyar da ba ta halas ba lokacin da yake mulki, inda ya ce ko taku daya ba shi da shi a wajen Najeriya. A wani labarin kuma, Shugaban ya ce babu wata kungiyar ’yan ta’adda da ta isa ta wargaza Najeriya. Shugaban Kasar ya bayyana haka ne yayin da ya kai ziyara fadar Sarkin Damaturu, Alhaji Hashumi Ibn Elkanemi II a fadarsa da ke garin Damaturu, ranar Talata. Buhari ya kuma bukaci ’yan Najeriya da su kara kaimi tare