Search This Blog
Saturday, 6 May 2023
Hukumar Lafiya ta Duniya ta ayyana karshen annobar Covid-19
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
Friday, 7 April 2023
Fiye da kashi 48 na al'ummar Afrika ba sa samun kulawar lafiya- WHO
Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta ce ‘yan Afrika miliyan 672 wanda ke wakiltar kashi 48 na al’ummar nahiyar basa samun kulawar lafiyar da ya kamata yayinda suke rayuwa cikin cutuka.
WHO ta ce dai dai lokacin da kasashe ke baje hajar gagarumin ci gaban da suka samu a bangaren kiwon lafiya, yayin bikin ranar Lafiya ta Duniya har yanzu Afrika na ganin mummunan koma baya a bangaren.
Daraktar hukumar WHO shiyyar Afrika Dr Matshidiso Moeti ta ce bangaren kiwon lafiya na ci gaba da samun koma baya a nahiyar wanda ke da nasaba da rashin kulawar shugabanni don habaka sashen.
A sanarwar da ta fitar a ranar lafiya ta Duniya wato World Health Day da ke gudana a kowacce ranar 7 ga watan Aprilu, shugabar ta WHO reshen Afrika, ta ce gazawar bangaren lafiya ya haddasa karuwar cutuka a sassan nahiyar da kuma tsanantar cutuka masu hadari.
Dr Matshidiso Moeti ta ce abin takaici yadda hatta kananun cutukan da basu kai su yi kisa ba, su ke iya kashe tarin jama’a a nahiyar ta Afrika saboda gurguncewar bangarorin kiwon lafiya.
A cewar jami’ar akwai karancin tsare-tsaren tafiyar da bangarorin kiwon lafiyar da kuma kin sanya kudi ga sashen kamar yadda ya kamata.
Haka zalika shugabar ta WHO a Afrika ta kuma koka da rashin kwararrun jami’an kiwon lafiya da kasashen nahiyar ke fama da kamfarsu.
Moeti ta bayyana cewa tasirin illar da annobar covid-19 ta yiwa nahiyar da kuma illolin dumamar yanayi da tuni kasashen nahiyar suka fara ganin tsanantarsu, sun sake wargaza kokarin kasashen na bunkasa bangaren lafiya.
RFI
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
Monday, 23 January 2023
Mutane biliyan biyar ka iya kamuwa da bugun zuciya a duniya
Hukumar Lafiya ta Duniya WHO ta ce, kimanin mutane biliyan biyar na fuskantar gagarumin hatsarin kamuwa da ciwon zuciya saboda cin abinci mai dauke da kitse da ta bayyana amatsayin gubaL
A shekarar 2018 ne, Hukumar Lafiyar ta Duniya ta yi roko da a kawar da cimakar da ke dauke da kitse ganin yadda mutane dubu 500 suka yi mutuwar-farar-daya a sassan duniya sakamakon wannan cimakar.
WHO ta ce, kasashen duniya 43 da ke dauke da jumullar mutane biliyan 2 da miliyan 800, sun dauki matakin daina kalace da irin wannan cimakar a kasashensu, amma har yanzu akwai mutanen duniya kimanin biliyan biyar da aka gaza ba su kariya a sassan duniya.
WHO ta ce, Masar da Australia da Koriya ta Kudu, na cikin kasashen duniya da suka yi watsi da gargadinta duk da cewa, su ke kan gaba a jerin kasashen da aka fi samun masu kamuwa da ciwon zuciya skamakon yawan cin abinci mai kitse.
Ana yawan cakuda wannan kitsen a cikin cimaka daban-daban da suka hada da man girki da abincin gwangwani da wasu kunsassun kayan kwalama.
Shugaban Hukumar Lafiya ta Duniya, Tedros Adhanom Ghebreyesus ya ce, irin wannan kitsen na dauke da sinadarin guba mai kisa , kuma ya kamata a daina amfani da shi a abinci.
Kamfanoni dai na sanya kitsen ne da zummar hana abinci lalacewa da wuri, sannan yana da saukin samu fiye da sauran sinadarai masu kara wa abinci tsawon wa’adin lalacewa.
(RFI)
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa
28 Arrested as Muhuyi Leads Drugs Crackdown
In a decisive operation to clamp down on drug-related criminality and protect communities, the Chairman of the Kano State Multi‑...
-
Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Godwin Emefiele, ya ce Bankuna za su ci gaba da karbar tsoffin takardun kudi na Naira ko da baya...
-
Matar hamshakin dan kasuwa na Kano, Alhaji Aminu Alasan Dantata, Hajiya Rabi ta rasu Jaridar SOLACEBASE ta rawaito cewa, Hajiya ...
-
Zababben Gwamnan Jihar Kano Ya Sanar Da Kwamitin Karbar Mulki …… Dr. Baffa Bichi, Abdullahi Musa ya nada a matsayin Shugaba da Sakatare Baya...

