Search This Blog

Showing posts with label Wutar lantarki. Show all posts
Showing posts with label Wutar lantarki. Show all posts

Tuesday, 8 August 2023

Gwamnatin Kano Za Ta Tallafawa Kamfanin TC Don Bunkasa Samar Da Wutar Lantarki A Kano-Dantiye

Gwamnatin jihar Kano ta himmatu wajen yin amfani da dukkan hanyoyin da za su bunkasa samar da wutar lantarki don ci gaban masana'antu.

A sanarwar da daraktan harkokin cikin gida na Ma'aikatar, Usman Bello ya sanyawa hannu, Ta tace Kwamishinan yada labarai Baba Halilu Dantiye ne ya bayyana hakan, a yayin da yake gabatar da jawabi a lokacin da ya karbi bakunci tawagar mataimakin Janaral Manaja na ofishin Kamfanin Dakon wutar lantarki dake Jahar Kano 

Kwamishinan ya ce Gwamna Abba Kabir a shirye yake ya ba hukumar TCN dauki domin kammala ayyukanta daban-daban a jihar.

Ya kuma yi nuni da cewa, babu wata gwamnati da za ta yi watsi da damar da za ta samar da wutar lantarki ga al’ummarta, duba da irin dabarun da take da shi wajen bunkasa harkokin tattalin arziki a jihar.

Daga nan sai Dantiye ya bada tabbacin GGM na goyon bayan ma’aikatar wajen fadakar da al’umma kan ayyukanta.

Tun da farko a nasa jawabin, Mataimakin Janaral Manaja na shiyyar Kano Muhammad Kamal Bello ya ce sun je ma’aikatar ne domin neman goyon bayan gwamnatin jihar Kano wajen gudanar da ayyukanta.

Ya bayyana cewa jihar Kano duk da yawan al’umma da tattalin arzikinta a kasar nan na da layukan sadarwa guda biyu kacal yayin da sauran jihohin ke da takwas.

Mal muhammad Kamal Bello ya ce akwai ayyukan watsa labarai da tashoshin sadarwa daban-daban da aka shafe sama da shekaru takwas ana aiwatarwa.

Ya daga cikin abubuwan da ke kawo cikas a ayyukan sun hada da rufe hanyoyin sadarwa da dama wadanda ke yaki da fadada layukan.

Sauran batutuwan sun hada da samar da filayen ayyukan kananan tashoshin Danbatta da Walalanbe da hukumar TCN ta bayar, in ji Mal Bello.

Daga nan sai ya yi kira ga gwamnati da ta sa baki wajen aiwatar da ayyukan.

Sunday, 30 April 2023

Wutar Lantarki: Katse Layin KEDCO A Kano Somin-Tabi Ne —TCN

Kamfanin Samar da Wutar Lantarki na Kasa (TCN) ya ce katse wutar da ya yi wa Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na KEDCO a Jihar Kano somin-tabi ne.

Wasu sassan Jihar Kano sun yi kwanaki a cikin duhu bayan TCN ya katse layin wutar da suke kai saboda taurin bashin da yake bin KEDCO.

TCN ya katse wasu layikan wutar KEDCO mai kula da jihohin Kano da Jigawa da Katsina bayan kokarinsa na ganin kamfanin ya biya bashin ya faskara.

Mataimakin Janar-Manajan TCN na Shiyyar Kano, Bello Muhammad da kuma kakakin KEDCO, Sani Bala Sani, sun tabbatar cewa TCN ya katse wutar a ranar 26 ga watan Afrilu da muke ciki.


Layukan wutar da TCN ya kashe a Kano su ne Club Road da CBN da kuma Flour Mills (Dan Agundi), wanda hakan ya jefa yankunan da ke samun wuta daga nan a cikin duhu na tsawon kwanaki.

Tun ranar 24 ga watan ranar 24 ga wata Babban Jami’in Kasuwanci na TCN, E. A. Eje ya sanar cewa, “TCN ya ba da umarnin katse wutar KEDCO saboda saba ka’idar biyan bashi.”

Ya bayyana cewa katse layikan somin-tabi ne kafin TCN ya katse wutar gaba daya idan kamfanin bai biya bashin ba.

Ya bayyana cewa katse layikan somin-tabi ne kafin TCN ya katse wutar gaba daya idan kamfanin bai biya bashin ba.


Ya ce, “Mun riga an sanar da KEDCO da duk wadanda ake bi bashi game da saba alkawarin nasu; Mun kuma wallafa a jarida inda muka bayyana ranar da za mu yanke musu wuta bisa tsarin kasuwancin, kuma har wa’adin ya wuce.”


Amma mai magana da yawun KEDCO, Sani Bala Sani, ya ce, “Duk da haka, kamfanin na aiki tare da TCN da sauran masu ruwa da tsaki domin ganin an daidaita nan ba da jimawa ba.”

Sani ya ba wa jama’a hakuri, da alkawarin tabbatar da sama musu wutar lantarki mai inganci.
AMINIYA 

Saturday, 7 January 2023

2023:Za Mu Sama Wa Katsina N10bn Daga Hasken Rana A Shekara —NNPP


Dan takarar Gwamnan Katsina a Jam’iyyar NNPP, Nura Khalil, yi alkawarin tara kudaden shiga Naira biliyan 10 daga hasken rana a duk shekara a jihar.

Injiniya Nura Khalil ya ce kudaden shigar N10bn da jihar za ta rika samu daga bangaren hasken rana zai sa ba sai ta jira daga Asusun Tarayya ba.

A gaggauta kammala masana’atar tiransfomar Najeriya —Buhari
A jawabinsa a taron fara yakin neman zabensa a Karamar Hukumar Mashi, ya ce, “Na fara da Mashi ne saboda da ita da Daurawa ta Jihar Jigawa da Kankiya bisa ga binciken da muka yi sun fi samar da hasken rana da za ta samar da lantarki ba sai an jira daga wani wuri ba.

“Za mu yi amfani da wannan hasken wutar lantarkin don sama wa jihar kudaden shigar da akalla za a samu bilyan N100 a shekara.


“Kudaden za mu yi amfani da su wajen gudanar da ayyukan gwamnati ba sai mun jira na Gwamnatin Tarayya ba.”

Ya kara da cewa idan ya ci zaben da ke tafe a watan Maris, “Muna da shirin kafa banki mallakar gwamnatin jiha wanda zai iya bayar da damar yin ajiya mai kama da shirin adashe don dai mu farfado da tattalin arzikin jihar.”

Game da matsalar tsaro, dan takarar ya ce Katsina tafi sauran jihohi hadari, amma idan NNPP ta hau mulki zai zama tarihi.

Ya kuma yi shagube ga wadanda yake zargi da sayen katinan zabe da nufin yin magudin zabe, da cewa a wannan karon karyarsu a kare.
“Ana bin mata ana sayen katunan zabensu a kan N10,000 amma a karshe sai a ba su N500.

“To a sani, babu batun magudi a wannan zaben, balle a ba wani katin wani ya je ya jefa kuri’a sama da goma,” in ji shi.

Ya zargi gwamnatin APC ta Jihar Katsina da yin watsi da fannin ilmi; inda ya ce a shekara bakwai na gwamnatin, yara 100,000 sun kasa rubuta jarabawa.

Don haka ya bukaci jama’a su zabi Jam’iyar NNPP don ta fitar da su daga kunci da rashin tsaron a jihar.
Tun da farko shugaban NNPP na jihar Katsina, Sani Liti ’Yankwani, ya ce, matsalolin satar jama’a, kisa da jahilci, sun ishi mutane hankali, saboda abin da ya kira rashin kulawar gwamnatin jihar.

A kan haka ne a ce idan aka zabi NNPP, za ta kawo karshen matsalolin musamman na rashin tsaro.

Shugaban NNPP na Kasa kuma dan takararta na shugaban kasa, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso wanda ya dan takarar Gwamnam Kano na jam’iyar, Abba Kabir Yusuf (Abba gida-gida) ya wakilta, ya ce, jam’iyy ta yi kyawawan tanade-tanaden samar da ayyukan yi da tallafin sana’o’i ga mata da matasa da kuma kawo karshen matsalar tsaro.
(AMINIYA) 


Friday, 6 January 2023

Jihohin Najeriya na neman Majalisar wakilai ta sa su cikin harkar samar da wuta

Kwamitin majalisar wakilan Najeriya da ke kula da harkokin wutar lantarki ya yi zama don jin ra'ayin jama'a, game da wani garambawul da majalisar ke shirin yi ga dokar lantarki domin bai wa jihohi damar shiga harkar samar da wuta.


Kwamitin ya ɗauki matakin ne bayan da jihohi suka nemi a basu damar shiga harkar a matakai daban-daban, da suka haɗa da samarwa da kuma rarrabawa.


Mahukunta a Najeriya dai sun sha nuna rashin gamsuwa da yadda kamfanonin wutar lantarkin suke gudanar da harkokinsu.


Honourable Magaji Ɗa'u Aliyu, shugaban kwamitin ya shaida wa BBC cewa "akwai kamfanin da ke ruwa da tsaki wajen tafiyar da harkokin wutar lantarki a ƙasar, sai dai ya ce jihohi a yanzu sun nemi a basu dama "su je su yi nasu".


"Mun saurare su, kuma sun kawo mana kundin da suka yi aiki a kai, za mu duba shi sannan kuma za mu faɗa musu halin da ake ciki a kai."

A cewarsa, gaba ɗaya jihohin Najeriya sun sa hannu a takardar da aka miƙa musu "har sun aiko da wakilai daga jihohi guda shida."shida.

Ban da gwamnatocin jihohi, ƙungiyoyi da wasu ɗaiɗaikun jama'a su ma sun bayyana nasu ra'ayin, kuma mafi yawa na nuna goyon baya ga yunƙurin da majalisar ke yi na gyaran fuska ga dokar wutar lantarkin.

Ita ma gwamnatin Najeriya a nata ɓangaren ta ce ta yi na'am da maganar garambawul ɗin sosai sakamakon rashin gamsuwar da ta yi da takun kamfanonin da aka damƙa wa samar da wutar lantarkin a halin da ake ciki.

Minista a ma'aikatar wutar lantarki a Najeriya, Mista Goddy Jedy Agba, ya bayyana cewa yin gyaran na da muhimmanci ga al'ummar ƙasar.

"Muna son gyaran, kowa na son wuta a Najeriya, idan an yi aikin sai mu samu ci gaba."

Ya ce akwai matakai na samar da wutar lantarki - samarwa da rarrabawa kuma a halin da ake ciki, gwamnati kawai tana samar da wutar ne kawai.

"A wannan shekara, za mu cire hannu daga samarwa, zai zama kowa zai taka rawa"

Kwamitin wutar lantarkin dai ya ce zai miƙa bayanan da ya tattara ga zauren majalisar wakilai, kuma a can ne za a yi tankaɗe da rairaya gabanin yanke shawara a kan abin yi.

Batun inganta wutar lantarki daɗaɗɗiyar magana ce a Najeriya, da aka yi yunƙuri daban-daban tun gabanin komawar ƙasar ga dimokraɗiyya, aka kuma ci gaba da kwan-gaba-kwan-baya har zuwa yau.

Kodayake za a iya cewa wutar da ake samarwa ta ƙaru a tsukin nan, amma kuma a ɓangare guda, ƴan ƙasar na kukan cewa ta yi ɗan karen tsada.

Tuesday, 3 January 2023

Gwamnatin Tarayya Da Gwamnonin 36 Sun Shiga Yarjejiniyar Sayar da Kamfanonin Wuta 5

 


A wata sanarwa da darekta janar na ofishin sayar da kaddarorin gwamnati wato BPE Alex Okoh ya fitar, ya nuna cewa za a sayar da kamfanonin wuta biyar a kwatan farko na wannan shekara da muka shiga, domin samar da kudade da za a cike gibin Kasafin kudin shekara 2023 da su.

Kasafin kudin na Naira Triliyan 21.82 ya zo da gibi har na kusan Naira triliyan 11 saboda rashin kudin shiga, haka ya sa aka samu gibin kashi 4.8 a ma'unin arzikin kasar wato GDP, wani abu da masanin tattalin arziki na kasa da kasa Shuaibu Idris Mikati ya nuna damuwa akan batun sayar da kamfanonin yana cewa akwai abin dubawa a wannan batun sayar da kamfanonin nan domin kar a sake fadawa cikin halin kakanakayi.

  • https://alheekmah.blogspot.com/2023/01/labari-da-dumiduminsa-yusuf-babangida.html
  • https://alheekmah.blogspot.com/2023/01/obasanjo-ya-zama-tamkar-dan-bakin-ciki.html

Mikati ya ce haka aka sayar da kamfanoni ga wadanda ba su da kudi a zamanin gwamnatin da ta shude, har suka gagara ba kasa wadataccen wuta. Mikati ya ce ya yi mamakin wai bankin UBA ne za sayar wa da kashi 60 na kamfanonin inda ya kira da a duba lamarin da idanun basira.

Kamfanonin da ke samar da wutan lantarki ( GENKOS) wadanda za a sayar sun hada da tashar wutar lantarki ta Geregu, da cibiyar samar da wutar lantarki mai karfin megawatt 562 a Calabar Jihar Kros Ribas da kuma cibiyar wutar lantarki ta Olorunsogo, amma ga mai fashin baki a al'amuran zamantakewa da gudanar da mulki Dokta Abdulrahaman Abu Hamisu ya ce wannan ya zo masa da mamaki domin ya kamata Najeriya ta yi damokradiya da gaske.

Abu ya ce matakin da ake dauka bai dace ba domin yana ba sai an sayar da kaddarori kafin a cike gibin kasafin kudi ba.

Abu ya ce ya kamata Najeriya ta yi koyi da wasu kasashe da suka cigaba wajen karban haraji maimakon sayar da kaddarori. Abu ya koka da yadda ake sace kudaden kasa ba tare da an kamo barayin ba. Ya kara de cewa idan ba a hanzarta samo hanyoyin kudaden shigowa ba, to da sauran rina a kaba, musamman yanzu da ake shirin zaben sabon gwamnati.

To sai dai ga tsohon mai ba ministan makamashi shawara a harkar gudanarwa, Idris Mohammed Madakin Jen yana mai ganin an dauki mataki mai kyau da zai kawo wa kasa wutar lantarki.

Idris ya ce dama kudaden na jihohi da kananan hukumomi ne, kuma lokaci ya yi da za a basu abinsu. Idris ya ce bankin UBA ce ta samo masu hannu da shuni da za su saye kamfanin samar da wutan lantarki musamman na birnin taraiyya Abuja.

Majalisar kula da harkokin kasuwanci ta kasa NCP ta amince da tsarin gudanar da aikin gina wani katafaren kamfani na dalar Amurka biliyan 3 da zai samar da wutan lantarki mafi girma a Afirka ta Yamma.

VOA

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

SAPZ Kano partners ABCOAD to organize FFS Training for Youth and Women.

The Special Agro-Industrial Processing Zones (SAPZ) Programme, Kano State, in collaboration with Audu Bako College of Agricultur...