Posts

Showing posts with the label Wutar lantarki

Gwamnatin Kano Za Ta Tallafawa Kamfanin TC Don Bunkasa Samar Da Wutar Lantarki A Kano-Dantiye

Image
Gwamnatin jihar Kano ta himmatu wajen yin amfani da dukkan hanyoyin da za su bunkasa samar da wutar lantarki don ci gaban masana'antu. A sanarwar da daraktan harkokin cikin gida na Ma'aikatar, Usman Bello ya sanyawa hannu, Ta tace Kwamishinan yada labarai Baba Halilu Dantiye ne ya bayyana hakan, a yayin da yake gabatar da jawabi a lokacin da ya karbi bakunci tawagar mataimakin Janaral Manaja na ofishin Kamfanin Dakon wutar lantarki dake Jahar Kano  Kwamishinan ya ce Gwamna Abba Kabir a shirye yake ya ba hukumar TCN dauki domin kammala ayyukanta daban-daban a jihar. Ya kuma yi nuni da cewa, babu wata gwamnati da za ta yi watsi da damar da za ta samar da wutar lantarki ga al’ummarta, duba da irin dabarun da take da shi wajen bunkasa harkokin tattalin arziki a jihar. Daga nan sai Dantiye ya bada tabbacin GGM na goyon bayan ma’aikatar wajen fadakar da al’umma kan ayyukanta. Tun da farko a nasa jawabin, Mataimakin Janaral Manaja na shiyyar Kano Muhammad Kamal Bello ya ce

Wutar Lantarki: Katse Layin KEDCO A Kano Somin-Tabi Ne —TCN

Image
Kamfanin Samar da Wutar Lantarki na Kasa (TCN) ya ce katse wutar da ya yi wa Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na KEDCO a Jihar Kano somin-tabi ne. Wasu sassan Jihar Kano sun yi kwanaki a cikin duhu bayan TCN ya katse layin wutar da suke kai saboda taurin bashin da yake bin KEDCO. TCN ya katse wasu layikan wutar KEDCO mai kula da jihohin Kano da Jigawa da Katsina bayan kokarinsa na ganin kamfanin ya biya bashin ya faskara. Mataimakin Janar-Manajan TCN na Shiyyar Kano, Bello Muhammad da kuma kakakin KEDCO, Sani Bala Sani, sun tabbatar cewa TCN ya katse wutar a ranar 26 ga watan Afrilu da muke ciki. Layukan wutar da TCN ya kashe a Kano su ne Club Road da CBN da kuma Flour Mills (Dan Agundi), wanda hakan ya jefa yankunan da ke samun wuta daga nan a cikin duhu na tsawon kwanaki. Tun ranar 24 ga watan ranar 24 ga wata Babban Jami’in Kasuwanci na TCN, E. A. Eje ya sanar cewa, “TCN ya ba da umarnin katse wutar KEDCO saboda saba ka’idar biyan bashi.” Ya bayyana cewa katse layikan so

2023:Za Mu Sama Wa Katsina N10bn Daga Hasken Rana A Shekara —NNPP

Image
Dan takarar Gwamnan Katsina a Jam’iyyar NNPP, Nura Khalil, yi alkawarin tara kudaden shiga Naira biliyan 10 daga hasken rana a duk shekara a jihar. Injiniya Nura Khalil ya ce kudaden shigar N10bn da jihar za ta rika samu daga bangaren hasken rana zai sa ba sai ta jira daga Asusun Tarayya ba. A gaggauta kammala masana’atar tiransfomar Najeriya —Buhari A jawabinsa a taron fara yakin neman zabensa a Karamar Hukumar Mashi, ya ce, “Na fara da Mashi ne saboda da ita da Daurawa ta Jihar Jigawa da Kankiya bisa ga binciken da muka yi sun fi samar da hasken rana da za ta samar da lantarki ba sai an jira daga wani wuri ba. “Za mu yi amfani da wannan hasken wutar lantarkin don sama wa jihar kudaden shigar da akalla za a samu bilyan N100 a shekara. “Kudaden za mu yi amfani da su wajen gudanar da ayyukan gwamnati ba sai mun jira na Gwamnatin Tarayya ba.” Ya kara da cewa idan ya ci zaben da ke tafe a watan Maris, “Muna da shirin kafa banki mallakar gwamnatin jiha wanda zai iya bayar da d

Jihohin Najeriya na neman Majalisar wakilai ta sa su cikin harkar samar da wuta

Image
Kwamitin majalisar wakilan Najeriya da ke kula da harkokin wutar lantarki ya yi zama don jin ra'ayin jama'a, game da wani garambawul da majalisar ke shirin yi ga dokar lantarki domin bai wa jihohi damar shiga harkar samar da wuta. Kwamitin ya ɗauki matakin ne bayan da jihohi suka nemi a basu damar shiga harkar a matakai daban-daban, da suka haɗa da samarwa da kuma rarrabawa. Mahukunta a Najeriya dai sun sha nuna rashin gamsuwa da yadda kamfanonin wutar lantarkin suke gudanar da harkokinsu. Honourable Magaji Ɗa'u Aliyu, shugaban kwamitin ya shaida wa BBC cewa "akwai kamfanin da ke ruwa da tsaki wajen tafiyar da harkokin wutar lantarki a ƙasar, sai dai ya ce jihohi a yanzu sun nemi a basu dama "su je su yi nasu". "Mun saurare su, kuma sun kawo mana kundin da suka yi aiki a kai, za mu duba shi sannan kuma za mu faɗa musu halin da ake ciki a kai." A cewarsa, gaba ɗaya jihohin Najeriya sun sa hannu a takardar da aka miƙa musu "har sun ai

Gwamnatin Tarayya Da Gwamnonin 36 Sun Shiga Yarjejiniyar Sayar da Kamfanonin Wuta 5

Image
  A wata sanarwa da darekta janar na ofishin sayar da kaddarorin gwamnati wato BPE Alex Okoh ya fitar, ya nuna cewa za a sayar da kamfanonin wuta biyar a kwatan farko na wannan shekara da muka shiga, domin samar da kudade da za a cike gibin Kasafin kudin shekara 2023 da su.   Kasafin kudin na Naira Triliyan 21.82 ya zo da gibi har na kusan Naira triliyan 11 saboda rashin kudin shiga, haka ya sa aka samu gibin kashi 4.8 a ma'unin arzikin kasar wato GDP, wani abu da masanin tattalin arziki na kasa da kasa Shuaibu Idris Mikati ya nuna damuwa akan batun sayar da kamfanonin yana cewa akwai abin dubawa a wannan batun sayar da kamfanonin nan domin kar a sake fadawa cikin halin kakanakayi. https://alheekmah.blogspot.com/2023/01/labari-da-dumiduminsa-yusuf-babangida.html https://alheekmah.blogspot.com/2023/01/obasanjo-ya-zama-tamkar-dan-bakin-ciki.html Mikati ya ce haka aka sayar da kamfanoni ga wadanda ba su da kudi a zamanin gwamnatin da ta shude, har suka gagara ba kasa wadataccen wuta.