Posts

Showing posts with the label Abba Gida Gida

Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Umarci Dukkanin Kwamishinonin Da Zai Nada, Su Bayyana Kadarorinsu

Image
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya umurci dukkan wadanda aka nada na kwamishinoni 19 su bi ka’idojin da’ar ma'aikata A sanarwar da babban sakataren Yada labaran Gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu, tace, da wannan sanarwar, ana sa ran wadanda aka zaba za su bayyana kadarorinsu a cikin mafi kyawun lokaci kafin a fara tantance su a majalisar dokokin jihar a ranar Alhamis 22 ga watan Yuni, 2023 da karfe 10 na safe a harabar majalisar dokokin jihar. Gwamnan ya sha alwashin cewa babu wani kwamishina da za a rantsar da shi a matsayin memba na majalisar zartaswa ta jihar ba tare da cike fom din bayyana kadarorinsa daga Ofishin hukumar kula da da'ar ma'aikata ba. "Duk sauran masu rike da mukaman siyasa a karkashin wannan gwamnati su ma za su bi umarnin da aka ba su." Gwamna Abba Kabir Yusuf na fatan jaddada aniyarsa ga mutanen jihar Kano nagari cewa gaskiya da rikon amana ya kasance tushen tsarin gwamnatinsa wanda za a yi amfani da shi wa

Gwamnan Kano Ya Zabi Tsohon Shugaban kungiyar Editoci Ta Kasa, Dantiye, Da Wasu 18 A Matsayin Kwamishinoni

Image
Gwamnan jihar KANO, Abba Kabir Yusuf wanda aka fi sani da Abba Gida Gida ya nada tsohon shugaban kungiyar Editocin Najeriya, Baba Halilu Dantiye, mni, da wasu mutane 18 a matsayin kwamishinoni da mambobin majalisar zartaswa ta jihar An zabi Dantiye a matsayin babban sakataren NGE a shekarar 2001, sannan ya yi wa’adi biyu a matsayin shugaban kasa, daga 2003 zuwa 2008. A zamaninsa ne aka fara gudanar da taron Editocin Najeriya, ANEC. Daga baya an haÉ—a taron a cikin Tsarin Mulki na Guild a matsayin taron shekara-shekara na wajibi. Haka kuma a cikin jerin sunayen akwai Ali Haruna Makoda, tsohon shugaban ma’aikata na tsohon gwamna Abdullahi Ganduje, da Nasiru Sule Garo, Gwamnan ya mika jimillar sunaye 19 ga majalisar domin tantance su. Kakakin majalisar, Hon. Jibril Ismail Falgore, ya fitar da sunayen yayin da yake karanta wasikar a zauren majalisar ranar Talata. Bayan karanta kudirin nadin da shugaban masu rinjaye na majalisar, Lawal Hussaini Chediyar Yangurasa (Dala) ya gabata