A sanarwar da babban jami’in tawagar tallafawa harkokin yada labarai ga hukumar NAHCON na kasa, Ibrahim Abubakar ya sanyawa hannu, yace, muna so mu sanarwa da jama’a musammam masu shirya wannan makirci, cewa shugaban hukumar NAHCON, Farfesa Abdullahi Sale Usman ba ya cikin wannan badakala da ta faru lokacin aikin Hajin 2024, a takaice shi an nada shi shugabancin hukumar ne watanni bayan gudanar da aikin aikin Hajin 2024.
Ibrahim ya ci gaba da cewa Zuwan Farfesa Abdullahi Saleh wajen taron jin ra’ayoyin jama’ar ya faeu ne sakamakon kasancewarsa shugaban hukumar a halin yanzu domin ya shaida yadda lamarin zai kasance kana kuma ya kara aniya domin fuskantar babban aikin dake gabansa a matsayin sabon shugaban hukumar
A saboda haka, muke kira ga masu shirya wannan makirci su guji aikata wannan mummunan aiki kan shugaban hukumar NAHCON