Posts

Showing posts with the label Karramawa

Ma'aikatan Asibitin Sansanin alhazai Na Kano, Sun Karrama Laminu Rabi'u Danbaffa

Image
Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jahar Alh, Laminu Rabi’u, ya yi alkawarin yin duk mai yiwuwa don ganin cewa alhazan jihar ba su fuskanci wahala ba a aikin Hajjin 2024  A sanarwar da jami’in hulda da jama’a na Hukumar, Yusuf Sulaiman Abdullahi Dederi ya sanyawa hannu, Ta Alh, Laminu Rabi’u ya bayyana haka ne a ranar Alhamis jim kadan bayan karbar lambar yabo ta ma’aikatan asibitin Hajj Camp a dakin taro na hukumar.  Alh, Laminu Rabi'u ya mika godiyarsa ga Gwamnan Jahar Alh Abba Kabir Yusif bisa jajircewarsa da kyautatawa Alhazan jihar. A nasa bangaren, Shugaban Hukumar Kula da Alhazai Alh Yusif Lawan, ya ce hukumar za ta ci gaba da baiwa ma’aikata duk wani taimako da ya kamata bisa la’akari da Gudunmawar da suke baiwa al’umma a lokacin gudanar da aikin Hajji. Alh, Yusif Lawan, ya yi kira gare su da su ba su hadin kai domin cimma burin da aka sanya a gaba. Da yake jawabi tun da farko, Jami'in dake lura da Asibitin Sansanin alhazai kuma Mataimakin Darakta