Posts

Showing posts with the label Ziyara

Shugaban NAHCON Ya Kai Ziyarar Neman Hadin Kai Ga Babban Limamin Legas Da Sauran Masu Ruwa Da Tsaki

Image
A ci gaba da ziyarar tuntubar da yake yi wa masu ruwa da tsaki a fadin kasar nan, shugaban riko/shugaban hukumar alhazai ta kasa (NAHCON), Malam Jalal Ahmad Arabi OON, FWC, ya kai ziyarar ban girma ga babban limamin Legas, Fadilat Sheikh Sulaiman Oluwatoyin. Abou Ola, da kungiyar Ansaru Deen Society of Nigeria. Da yake jawabi a wajen taron, shugaban NAHCON ya ce ya yanke shawarar ziyartar malamin da kungiyar musulmi ne domin neman goyon bayansu da hadin kai a kokarin da hukumar ke yi na yi wa al’ummar kasa hidima musamman mahajjata. A sanarwar da Mataimakin daraktan yada labarai da dab'i na Hukumar, Mousa Ubandawaki ya sanyawa hannu, Shugabn a  cewarsa, ya zama wajibi shugabannin musulmi su tashi tsaye wajen wayar da kan alhazai a wani bangare na ayyukansu na mishan kamar yadda Allah Madaukakin Sarki ya yi umarni da su. “Na zo nan ne domin in tunatar da malamanmu da shuwagabanninmu ayyukansu na addini da su taimaka wajen ilimantar da al’ummarmu, ba za mu iya yin watsi d

Na kai Ziyara Ga Malaman Addinin Musulinci Ne Domin Karfafa Dangantaka Da Masu Ruwa Da Tsaki - Shugaban NAHCON

Image
Mai rikon Shugabancin Hukumar Hajji ta Kasa (NAHCON), Malam Jalal Ahmad Arabi, OON, FNC ya bayyana cewa ziyarar da ya kai ga fitattun shugabanni da malaman addinin Musulunci na daga cikin shirin tuntubar juna domin karfafa kokarin hukumar wajen samun nasara baki daya. kawai a lokacin Hajjin 2024 amma bayan haka. A cewarsa, samun nasarar aikin Hajji wani nauyi ne na hadin gwiwa don haka duk mai ruwa da tsaki a harkokin aikin Hajji dole ne a ci gaba da gudanar da aiki tare domin samun nasara. A sanarwar da Mataimakin daraktan hulda da jama'a da Dab'i, Mousa Ubandawaki ya sanyawa hannu, ya bayyana cewa ba za a iya karasa rawar da shugabannin Musulunci ke takawa ba domin suna taka muhimmiyar rawa wajen samun nasara ko akasin haka a kasar nan. Don haka ya nemi goyon bayansu da ba da hadin kai wajen ganin an cimma manufar inganta ayyukan alhazan Najeriya. "Za a iya samun nasara ta hanyar tuntuba da aiki tare", in ji shi. Ku tuna cewa Shugaban/Shugaban ya yi alka

Wike Ya Ziyarci Ganduje A Ofishin APC

Image
Tsohon Gwamnan Jihar Ribas, wanda aka tantance domin zama minista, Nyeson Wike, ya ziyarci Shugaban Jam’iyyar APC mai mulki, Abdullahi Umar Ganduje a ofishin jam’iyyar. Ganduja ya karbi bakuncin Wike a ofishinsa ne yayin da ake rade-radin yana shirin sauya sheka daga jam’iyyarsa ta PDP zuwa APC. Sai dai ya sha musanta shirin komawa jam’iyyar mai mulki. Wike wanda Shugaba Bola Ahmed Tinubu na APC ya mika sunansa a cikin jerin ministocin da zai nada ya fito karara ya yaki dan takarar shugaban kasan PDP a zaben 2023, Atiku Abubakar. A yayin wani bikin da aka shirya masa bayan ya mika mulki ga zababben gwaman jiharsa, Simi Fubara, an ji gwamnan na rokon Wike kada ya yi watsi da shi idan ya dawo jam’iyya mai mulki. Rade-radin komawar Wike jam’iyyar APC sun kara karfi ne bayan Shugaba Tinubu ya mika sunansa a jerin ministocinsa. Shugabannin PDP dai sun bayyana rashin jin dadinsu, tare da kurarin daukar mataki a kan tsohon gwamnan na Ribas. (AMINIYA)