Cikin sanarwar da ya wallafa a shafinsa na #Facebook, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya ci gaba da "A cikin watanni masu zuwa, za a fitar da ƙarin bayani, kuma za a fara aikin tantancewa domin fara wannan aiki.
Haka kuma, za a buɗe makarantun fasaha guda 44 da Makarantun koyon Ilimin Addinin Musulunci guda 44 da ke fadin kananan hukumominmu da Gwamnatin Sanata Kwankwaso ta kafa, wadanda gwamnatin da ta gabata ta rufe kuma ta yi watsi da su domin ci gaba da karatu da.