Search This Blog

Showing posts with label Aisha Buhari. Show all posts
Showing posts with label Aisha Buhari. Show all posts

Wednesday, 10 May 2023

Mu Tashi Tsaye Domin Kawo Karshen Rikicin Sudan — Aisha Buhari

Uwargidan Shugaban Najeriya, Aisha Buhari ta roki a hada karfi da karfe don ganin kurar rikicin Sudan ta kwanta.

Jaridar Premium Times ta ruwaito Aisha Buhari na wannan kira a wani taro da ta jagoranta jiya Litinin a Fadar Gwamnati da ke Abuja.

A cewar jaridar, Aisha Buhari na ganin akwai rawar da matan shugabannin Afirka za su iya takawa musamman wajen kai agaji Sudan.
Sama da mutane 500 ake kyautata zaton cewa rikicin ya yi sanadin rasuwarsu kawo yanzu.

Mutum sama 700,000 sun rasa muhallansu

Alkaluman mutanen da rikicin Sudan ya raba da muhallansu ya ninka zuwa sama da mutum 700, 000, a cewar Majalisar Dinkin Duniya.

Karuwar mutanen da ke guje wa muhallansu ya sanya fargaba kan yaduwar fadan duk da tattaunawar tsagauta bude wuta da ake yi a Saudiyya.

Khartoum na da al’umma kusan miliyan 5.4, sai dai an daidaita birnin mai cike da zaman lafiya a baya tun bayan barkewar fada a ranar 15 ga watan Afrilu.

Tun ranar 15 ga watan Afrilu, yaki ya barke a Sudan kuma har wannan lokaci, an kasa cimma yarjejeniyar tsagaita wuta ta dindindin.
Khartoum na da al’umma kusan miliyan 5.4, sai dai an daidaita birnin mai cike da zaman lafiya a baya tun bayan barkewar fada a ranar 15 ga watan Afrilu.

Ana gudanar da fadan ne tsakanin sojojin kasar da Janar Abdel Fattah al-Burhan ke jagorata da kuma dakarun RSF bangaren Janar Mohamed Hamdan Dagalo, wanda aka fi sani da Hemedti.

Sama da mutum 600 ne aka kashe kawo yanzu tare da jikkata 5,000.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...