Posts

Showing posts with the label Aisha Buhari

Mu Tashi Tsaye Domin Kawo Karshen Rikicin Sudan — Aisha Buhari

Image
Uwargidan Shugaban Najeriya, Aisha Buhari ta roki a hada karfi da karfe don ganin kurar rikicin Sudan ta kwanta. Jaridar Premium Times ta ruwaito Aisha Buhari na wannan kira a wani taro da ta jagoranta jiya Litinin a Fadar Gwamnati da ke Abuja. A cewar jaridar, Aisha Buhari na ganin akwai rawar da matan shugabannin Afirka za su iya takawa musamman wajen kai agaji Sudan. Sama da mutane 500 ake kyautata zaton cewa rikicin ya yi sanadin rasuwarsu kawo yanzu. Mutum sama 700,000 sun rasa muhallansu Alkaluman mutanen da rikicin Sudan ya raba da muhallansu ya ninka zuwa sama da mutum 700, 000, a cewar Majalisar Dinkin Duniya. Karuwar mutanen da ke guje wa muhallansu ya sanya fargaba kan yaduwar fadan duk da tattaunawar tsagauta bude wuta da ake yi a Saudiyya. Khartoum na da al’umma kusan miliyan 5.4, sai dai an daidaita birnin mai cike da zaman lafiya a baya tun bayan barkewar fada a ranar 15 ga watan Afrilu. Tun ranar 15 ga watan Afrilu, yaki ya barke a Sudan kuma har wannan loka