Posts

Showing posts with the label Gabon

Mutanen Gabon Sun Yaba Da Juyin Mulkin Da Sojoji Suka Yi

Image
Shugaban Kasar Ƙasar Gabon, Ali Bongo ya buƙaci ƙasashen duniya su kawo ɗauki bayan sojojin ƙasar sun yi masa juyin mulki. Sojojin sun tsare Ali Bongo a Fadar Shugaban Kasa, inda daga nan ake kyautata zaton ya fitar da saƙon bidiyon da yake neman ɗaukin. “Ina kira ga duk abokan ƙasarmu a faɗin da cewa su yi magana a kan abin da ke faruwa (…) kan waɗannam mutane da suka tsare Ni tare da iyalaina.” in ji shi a cikin bidiyon da aka gan shi cikin tsananin.Kawo yanzu dai ba a iya tantance yadda aka yi bidiyon ya fito ko sahihancinsa ba.Karon farko ke nan da aka ji ɗuriyar Bongo wanda sojoji suka hamɓarar ’yan sa’o’i bayan ya lashe zaɓen da zai fara wa’adin mulkinsa na uku. Idan juyin mulkin Gabon ya tabbata, zai zama na takwas da sojoji suka yi cikin shekara uku a nahiyar Afirka, kuma duk ƙasashen da Faransa ta raina a baya. (AMINIYA)