Posts

Showing posts with the label Bude Ayyuka

Labari da dumiduminsa : Tinibu Zai Zo Kano Domin Bude Ayyuka - Ganduje

Image
Gwamnan jihar kano Dr Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewa ana sa ran zaɓaɓɓen shugaban ƙasa Bola Ahmad Tinubu zai zo jihar kano domin bude wasu aiyuka da gwamnatinsa gudanar a nan kano.   ” A yayin da muka cigaba da bude wasu daga cikin aiyukan raya kasa da gwamnatinmu ta yi a kwarya birnin kano da kewaye, Muna sa rana Zaɓaɓɓen Shugaban kasa Asiwaju Bola Ahmad Tinubu zai zo Kano domin kaddamar da sabuwar gadar da muka Samar a kofar mata zuwa Ibrahim Taiwo Road”. Kadaura24 ta rawaito Ganduje ya bayyana hakan ne yayin da yake jagorantar taron majalisar zartarwar ta jihar kano na wannan makon a gidan gwamnatin jihar kano. Ganduje yace ya bude aiyuka Masu tarin yawa Kuma zai cigaba da bude aiyukan don raya kasa da gwamnatinsa ta gudanar. Ganduje dai ya na bude aiyukan da ya gudanar ne a wani bangare na bankwana ga al’ummar jihar kano sakamakon karewar wa’adin gwamnatin sa a ranar 29 ga watan mayu.

Bude Ayyuka: Gwamna Ganduje Ya Tabbatar Da Aika Wasikar Zuwa Fadar Shugaban Kasa Domin Dage Ziyarar

Image
 - A matsayin 'yan majalisa, masana, shugabannin siyasa, 'yan kasuwa sun yanke shawara Cikin tsananin damuwa da wahalhalun da ke tattare da karancin lokacin da babban bankin Najeriya CBN ya bayar na dakatar da amfani da tsofaffin kudaden Naira, da kuma dalilan tsaro, gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya bayyana cewa jihar ta warware tare da rubutawa fadar shugaban kasa cewa, ziyarar shugaban kasa domin kaddamar da wasu ayyuka an dage shi. Ya bayyana haka ne a lokacin da yake tattaunawa da masana da ‘yan majalisar dokoki da shugabannin siyasa da ‘yan kasuwa a jihar a gidan gwamnati da ke Kano a ranar Juma’a, inda ya ce an dauki matakin ne domin kaucewa duk wani yanayi na rashin tabbas. “A yayin da muke jiran wannan ziyara mai muhimmanci, mun tsinci kanmu a cikin wannan hali, wanda ya jefa ‘yan kasa cikin wahalhalu, saboda dalilan tsaro mun rubutawa fadar shugaban kasa cewa a dage ziyarar shugaban kasa Muhammadu Buhari a Kano. Cikin sanarwar da babban sakata