Posts

Showing posts with the label PDP

Hadakar Jam'iyyun Siyasa A Kano Sun Kauracewa Zanga-zangar Matsin Rayuwa Da Ake Shirin Yi

Image
Jam’iyyar NNPP mau mulki da na adawa da suka haɗa da APC da PDP a unguwar Dakata, Ƙaramar Hukumar Nassarawa a jihar Kano sun haɗa kai wajen kauracewa zanga-zangar da ake shirin yi kan matsin rayuwa a fadin kasar nan. Jam’iyyun, ta bakin ciyamonin su na ƙaramar hukumar, sun yi kira ga al’umma da su kauracewa shiga zanga-zangar. A wani taron gangami da aka yi a Dakata Gidan Dagaci a jiya Asabar, Sabo Sambo (NNPP) da Umar Usman Usman (APC) da na PDP sun gargadi matasa akan illar da zanga-zangar ka iya haifar wa. A cewar su, akwai sauran hanyoyi da kundin tsarin mulkin ƙasa ya bayar domin neman hajji da yanci daga gwamnati sama da zanga-zanga. Sun nuna cewa gwamnatin jihar Kano da ta taraiya gana daya shekarar su daya akan mulki, inda su ka kira al’umma da su yi musu uzuri. “Musamman ma idan aka yi duba na tsanaki za a ga cewa gwamnatin Tinubu da ta jihar Kano, a shekara ɗaya da su ka yi a mulki, sun yi abubuwan yaba wa. “Za ku ga cewa a bangaren aiyukan lafiya da ilimi da noma

Labari Da Dumiduminsa: 'Yan Majlisar Jahar Rivers 27 Masu Biyayya Ga Wike Sun Bar PDP Zuwa Jam'iyyar APC

Image
Akalla ‘yan majalisar dokokin jihar Ribas 27 cikin 32 ne suka sauya sheka daga jam’iyyar PDP zuwa jam’iyyar APC, sakamakon rikicin da ya barke tsakanin gwamnan jihar Ribas, Siminalayi Fubara da ministan babban birnin tarayya (FCT). Nyesom Wike ya zurfafa. Wani dan majalisar, Enemi George, ya tabbatar wa gidan talabijin na Channels cewa ‘yan majalisar 27 na karkashin jagorancin Martin Amaewhule ne. 'Yan majalisar sun yanke Wannan hukuncin ne a yayin zamansu na safiyar ranar Litinin (DailyNews24)

Kotu Ta Kwace Kujerar Sanatan APC A Kogi, Ta Ba Natasha Ta PDP

Image
Kotun Daukaka Kara ta Ayyana Natasha Akpoti ta jam’iyyar PDP a matsayin halastacciyar wacce ta lashe zaben kujerar Sanatan Kogi ta Tsakiya. Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) dai a watan na Fabrairu ta ayyana Sanata Abubakar Ohere na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya lashe zaben, amma Natasha ta garzaya kotu. Daga bisani dai kotun sauraron kararrakin zabe da ke Jihar Kogi ta soke zaben na Ohere, sannan ta tabbatar mata da nasara. Kotun dai, wacce Mai Shari’a K.A Orjiakor ya jagoranta, ta ce an yi wa Ohere aringizon kuri’u a wasu rumfunan zabe tara da ke Karamar Hukumar Ajaokuta. Alkalin ya ce an kuma cire sakamakon Natasha a mazabun da karin wasu guda uku, duka dai a cikin Karamar Hukumar. Hakan ne ya sa kotun ta ayyana ta a matsayin wacce ta lashe zaben da kuri’u sama da 54,074, sabanin kuri’a 51,291 da ta ce Ohere ya samu. Sai dai Sanatan bai gamsu da hukuncin ba, inda daga bisani ya garzaya kotun daukaka karar, amma ta tabbatar da hukuncin kotun bayan. (AMINIYA)

Jami'an Tsaro Sun Rufe Ofishin PDP Na Jahar Ondo

Image
Jami’an Hukumar Tsaro ta DSS da kuma ’yan sanda sun rufe sakatariyar jam’iyyar adawa ta PDP ta Jihar Ondo. Hukumomin tsaron sun dauki matakin ne a safiyar Litinin a daidai lokacin da al’ummar jihar suke gunaguni da neman gwamnatin jihar ta bayyana musu inda Gwamna Rotimi Akeredolu yake da kuma halin da yake ciki. Yadda Ba Da Dala Ga Masu Shigo Da Shinkafa Zai Shafi Farashin Ta Gida Ganduje ya lashi takobin kare kujerar gwamnan Nasarawa da kotu ta kwace Ana zargin hukumomin tsaron sun rufe ofisihin jam’iyyar ne sakamakon shirin wasu ’yan jam’iyyar na gudanar da zanga-zanga kan rashin kasancewar gwamnan a jihar na tsawon lokaci. Da farko Gwamna Akerodule wande ke fama da rashin lafiya da ba a bayyana ba, ya shafe wata uku a kasar Jamus, inda yake jinya, kafin ya dawo jihar a watan Satumba. Tun bayan dawowar gwamnan, ya ci gaba da zama a gidansa, da ke birnin Ibadan, babban birnin Jihar Oyo, lamarin da ya sa babbar jam’iyyar adawa ta PDP a jihar kiraye-kirayen ya sauka daga mu

PDP Ta Bukaci Sanyawa Buhari Takunkumi

Image
Babbar jam’iyyar adawar Najeriya ta PDP ta bukaci kasashen duniya da su hana shugaban kasa Muhammadu Buhari bizar tafiye tafiye da zaran ya mika mulki ranar 29 ga watan gobe, saboda abinda ta kira kalamansa dangane da zaben shugaban kasar da akayi ranar 25 ga watan Fabarairu.  Yayin tsokaci akan zaben, Buhari ya bayyana ‘yan adawar Najeriya a matsayin wadanda suka shantake akan cewar zasu samu nasara ba tare da neman goyan bayan jama’a kamar yadda jam’iyarsa ta APC tayi ba.  Sakataren hulda da jama’a na jam’iyyar Debo Ologunagba yace kalaman shugaban na iya tinzira jama’a da kuma haifar da illa ga zaman lafiyar kasar.  Ologunagba ya kuma ce kalaman na iya karfafawa alkalai gwuiwa wajen yanke hukunci akan karar da suka shigar a gaban kotu domin kalubalantar sakamakon zaben wanda yace tuni wasu a ciki da wajen kasar ke bayyana shi a matsayin mafi muni a tarihin Najeriya.  Jam’iyyar PDP tace zaben da akayi bana ya gamu da matsalolin da suka sabawa kundin tsarin mulkin kasa da

Gobara Ta Barke A Gidan PDP

Image
  Ga dukkan alamu gobara ta sake barkewa a gidan babbar jam’iyyar adawa ta kasar nan wato PDP, wadda ta sake shiga rudu, makonni kadan da faduwarta a zaben Shugaban Kasa. A ranar Talata da ta gabata ce, Kwamitin Zartarwar Jam’iyyar na Kasa (NWC), ya ayyana Ambasada Iliya Umar Damagum a matsayin Shugaban Riko na jam’iyar ta kasa. Kafin nadinsa, Alhaji Iliya Damagum shi ne Mataimakin Shugaban Jam’iyyar PDP na kasa Shiyyar Arewa. Kakakin Jam’iyyar PDP, Debo Ologunagba ne ya bayyana nada Damagun a ranar Talata a wani taron manema labarai a Abuja. A sanarwar da PDP ta fitar, ta ce ya zame mata dole ta yi biyayya ga umarnin wata kotu da ta bukaci Shugaban Jam’iyyar na Kasa Dokta Ayu Iyorchia ya daina bayyana kansa a matsayin shugaban jam’iyyar har zuwa lokacin da za ta yanke hukunci kan kararsa da aka kai gabanta. Wata Babbar Kotu a Jihar Benuwai ce ta dakatar da Dokta Iyorchia Ayu daga shugabancin Jam’iyyar PDP ta Kasa. Alkalin Kotun, Mai Shari’a W.I Kpochi ne ya bayar da umarnin a ranar Li

Labari da dumiduminsa : Kotun Daukaka Kara Ta Tabbatar Da Sadiq Wali A Matsayin Dan Takarar Gwamnan Kano Na PDP

Image
A ranar Juma’a ne wata kotun daukaka kara ta jihar Kano ta tabbatar da Sadiq Aminu Wali a matsayin dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP a Kano. A wani hukunci na bai daya da ta yanke a ranar Juma’a, kotun daukaka kara ta yi watsi da hukuncin da karamar kotun ta yanke na tabbatar da Muhammad Abacha a matsayin dan takarar gwamnan jihar Kano na PDP. Cikakkun labarin zai zo muku nan ba da jimawa ba…

Kotun Koli ta sake tabbatar da Hajiya Laila Buhari a matsayin 'Yar Takarar Sanatan PDP Ta Kano Tsakiya

Image
A ranar Alhamis ne kotun koli ta sake tabbatar da Hajiya Laila Buhari a matsayin ‘yar takarar Sanatan Kano ta tsakiya a jam’iyyar PDP. SOLACEBASE ta ruwaito cewa a baya kotun daukaka kara ta tabbatar da Laila Buhari ta soke zaben Danburan Nuhu. Kotun kolin da ta yanke hukuncin da mai shari’a Muhammad Lawal Garba ya karanta, ta yi watsi da dukkan dalilan daukaka kara ta Danburam Nuhu. Jastis Garba na tare da Jastis Kudirat Kekere Ekun, da Jastis Saulawa da Jastis Ibrahim Jauro, da Jastis Emmanuel Agim Cikakken labarin zai zo muku nan gaba 

2023PDP Ce Ta Haifar Da Wahalar Man Fetur A Najeriya – Tinubu

Image
Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, Bola Tinubu ya ce dillalan man da PDP ta bai wa lasisi zamanin mulkinta ne ke boye fetur yanzu a Najeriya. Tinubu ya kuma ce magoya bayan PDPn da jam’iyyar ta bai wa lasisin zamanin mulkinta ne ke yin hakan saboda dalilan siyasa da kuma haddasa dogayen layuka a gidajen mai. Idan muka je saro kaya da tsoffin kudi ba a karba – ’Yan kasuwar Gombe ‘Duk Shugaban Kasar da zai zo zai fuskanci kalubale irin na Jonathan da Buhari’ Tinubu ya bayyana hakan ne yayin gangamin yakin neman zabensa da ya gudanar a Jihar Binuwai ranar Alhamis. Ya ce, PDP Jam’iyya ce ta ruruta wutar talauci ce, musamman idan aka yi la’akari da yadda ’yan Najeriya ke shan bakar wahala a yanzu. Sun bai wa magoya bayansu lasisin da yanzu ya haifar da dogayen layuka na jabu a gidajen mai. PDP haka ya ishe ku fa!” Ya kuma ce rashin sanin doka ne ya sanya abokin hamayyarsa, Atiku Abubakar, ya ce kasuwancin sufuri yake a lokacin da yake aiki da Hukumar Hana Fasakwauri ta

Duk Mai Son Mukami A Gwamnanatina Sai Ya Kawo Akwatinsa Lokacin Zabe - Atiku

Image
Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya ce duk dan jam’iyyar da ke neman kwagila ko mukami a gwamnatinsa, sai ya nuna sakamakon zaben mazabarsa kafin a ba shi. Atiku ya bayyana hakan ne ranar Laraba a Abekuta babban birnin Jihar Ogun, yayin taron ganawa da masu ruwa da tsaki na jam’iyyar. Atiku ya ce halartar kowanne yakin neman zaben jam’iyyar ba shi ne tabbacin samun matsayi ko kwangila a gwamnatinsa ba, jajircewa wajen ganin an kawo akwatinan mazaba ne. Tsohon Mataimakin Shugaban Kasar ya kuma ce, “Dukkanku magoya bayan PDP ne, kuma kuna so ta dawo mulki, don haka ina rokonku ku tabbatar kun kawo akwatinan mazabunku. Yawon zuwa yakin neman zaben kafatanin ’yan takarar jam’iyya ba shi ne zai sa ka samu aiki ko matsayi ko kwangila ba idan an ci zabe, hanyar da kadai za ku samu shi ne nuna min sakamakon zaben mazabarku. “Kuma ina bai wa kowanne dan takarar PDP umarnin yin hakan, domin da haka ne kadai za mu ci zabe. Atiku ya kuma yi alkawarin farfado