Search This Blog

Showing posts with label NDC. Show all posts
Showing posts with label NDC. Show all posts

Tuesday, 1 September 2026

Jiga-jigan NDC magoya bayan Gawuna na shirin komawa APC

……Sun kai ziyarar nuna goyon baya ga Gwamna Yusuf da Mataimakinsa

Wasu daga cikin jiga-jigan jam’iyyar NDC da ake alakanta su da tsohon Mataimakin Gwamnan Kano, Nasiru Yusuf Gawuna, sun fara shirye-shiryen komawa jam’iyyar APC.

Tawagar ta kai ziyarar nuna goyon baya ga Gwamnan Kano, Abba Kabir Yusuf, da Mataimakinsa, Murtala Sule Garo, a wannan Talatar da yamma.

Tawagar, wadda babban aminin Gawuna, Hon. Muhammad Badaru Umar, ya jagoranta, ta ƙunshi Hon. Ali Datti Yako, Mataimakin Shugaban NDC na Jihar Kano; Hon. Mansur Isa Gawuna; Hon. Uba Tanko Mijinyawa (Uba Danzainab); Hon. Aminu Umar Faruk; Hon. Sani Jibrin; Hon. Salisu Muhammad; Hon. Musa Sani Indabo; Hon. Muhammad Kabir Bala; Hon. Hassan Abba Abdullahi da Comrade Abdurrahman Muhammad.

Da yake bayani kan dalilin ziyarar, Hon. Muhammad Badaru Umar ya ce ƙaunar ci gaban Jihar Kano ce ta sa suka ga ya dace su gana da Gwamna Abba Kabir Yusuf.

Ya ce suna son ganin Kano ta ci gaba, yana mai bayyana ziyarar a matsayin wani ɓangare na tuntuba da tattaunawa kan makomar siyasa da ci gaban jihar.

A nasa bangaren, Hon. Ali Datti Yako ya ce kowa ya san irin ƙoƙarin da Gwamna Abba Kabir Yusuf ke yi wajen sauya fasalin Kano.

“Dukkanmu mun san cewa Gwamna Yusuf yana aiki tuƙuru wajen sauya fasalin Kano,” in ji Ali Datti Yako.

Ziyarar na zuwa ne a daidai lokacin da ake samun sauye-sauyen siyasa a Kano, yayin da manyan ’yan siyasa ke ci gaba da sake tsara matsayinsu gabanin zaɓen 2027.

Ana ganin shirin komawar waɗannan jiga-jigai zuwa APC a matsayin wani babban sauyi da zai iya ƙara wa jam’iyyar ƙarfi a Kano.

Sai dai, kawo yanzu, tawagar ba ta bayyana takamaiman ranar da za ta ayyana komawarta APC a hukumance ba.


NDC loses bigwigs in Kano as Gawuna’s team set to rejoin APC

…… Pays solidarity visit to Governor Yusuf and his Deputy

A team loyal to former Kano State Deputy Governor, Nasiru Yusuf Gawuna, has paid a solidarity visit to Governor Abba Kabir Yusuf and his Deputy, Comrade Murtala Sule Garo, ahead of their planned defection from the National Democratic Congress (NDC) to the All Progressives Congress (APC).

This was contained in a statement issued by the governor’s spokesman, Sunusi Bature Dawakin Tofa, on Tuesday.

The team, led by a close ally of Gawuna, Hon. Muhammad Badaru Umar, included Hon. Ali Datti Yako, NDC Vice Chairman, Kano State; Hon. Mansur Isa Gawuna; Hon. Uba Tanko Mijinyawa (Uba Danzainab); 

Others include Hon. Aminu Umar Faruk; Hon. Sani Jibrin; Hon. Salisu Muhammad; Hon. Musa Sani Indabo; Hon. Muhammad Kabir Bala; Hon. Hassan Abba Abdullahi; and Comrade Abdurrahman Muhammad.

Speaking during the visit, Hon. Muhammad Badaru Umar said their decision to meet Governor Yusuf was driven by their passion for the development and progress of Kano State.

He said the team considered it necessary to engage with the Governor and his Deputy as part of their consultations and efforts towards contributing to the development of the state.

On his part, Hon. Ali Datti Yako said the people of Kano are aware of the efforts being made by Governor Abba Kabir Yusuf to transform the state.

“Everyone knows that Governor Yusuf is working tirelessly to transform Kano State,” he said.

The visit comes amid ongoing political realignments in Kano ahead of the 2027 general elections, with prominent political figures continuing to reassess their political affiliations.

The anticipated return of members of Gawuna’s political team to the APC is expected to further strengthen the party in Kano, particularly as preparations for the 2027 elections gather momentum.

The delegation also expressed solidarity with Governor Yusuf and his Deputy, Murtala Sule Garo, reaffirming their interest in the continued development and progress of Kano State.


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Jiga-jigan NDC magoya bayan Gawuna na shirin komawa APC

……Sun kai ziyarar nuna goyon baya ga Gwamna Yusuf da Mataimakinsa Wasu daga cikin jiga-jigan jam’iyyar NDC da ake alakanta su da...