Posts

Showing posts with the label Jahar Nassarawa

Kotun Koli Ta Tabbatar Da Gwamna Abdullahi Sule A Matsayin Gwamnan Jahar Nassarawa

Image
Kotun Koli ta yi watsi da karar da dan takarar gwamna na jam’iyyar PDP, David Umbugadu, ya shigar kan zaben Gwamna Abdullahi Sule na Jihar Nasarawa. Kotun ta kori karar kan rashin cancanta, amma ba ta ci tarar dan takarar na jam’iyyar PDP ba. Cikakken bayani na tafe…

Bakuwa Ta Sace Jariri Awa 3 Da Haihuwarsa A Asibiti

Image
  Ana zargin bakuwa ta sace jaririn ne da hadin bakin ’yar uwar mai jegon Wata mata ta sace jariri awa uku bayan haihuwarsa a Asibitin Kwararru na Dalhatu Arafat (DASH) da ke garin Lafia, Jihar Nasarawa. Ana zargin bakuwar ta sace jaririn ne da hadin bakin ’yar uwar mai jegon sa’o’i kadan da haihuwarsa ta hanyar yi wa mahifiyarsa tiyata. Aminiya ta gano bayan haihuwarsa da misalin karfe 3 na asubahin ranar Talata ne jami’an asibiti suka mika jaririn da mai jegon ga wata ’yar uwarta domin ta ci gaba da kula da su. Wani ganau da ya nemi a boye sunasa ya ce, bayan sun dawo dakin masu jego ne ’yar uwar mai jegon ta kawo mata da wata bakuwa, wadda ake zargin sun hada baki wajen sace jaririn. ‘Kamar Layar Zana’ A cewarsa, “’yar uwar mai jegon ce ta ce mata za ta koma gida ta dauko cajar wayarta da ta manta; shi ne ta hada ta da wata mata da za ta zauna da su kafin ta dawo ,” wadda ake zargin ita ce ta sace jaririn. Sace jaririn daga dakin masu jegon da misalin karfe 6 na safe,  awa uku da ha

Yanzu-Yanzu: Kotun Daukaka Kara Ta Tabbatar Da Zaben Gwamna Abdullahi Sule Na Jahar Nassarawa

Image
Kotun daukaka kara da ke Abuja ta tabbatar da zaben gwamnan jihar Nasarawa, Abdullahi Sule.  Kotun daukaka kara ta kuma yi watsi da hukuncin da kotun sauraron kararrakin zabe ta jihar Nasarawa ta yanke a ranar 2 ga watan Oktoba da ta kori Sule na jam’iyyar APC tare da bayyana David Ombugadu, dan takarar jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya lashe zaben gwamna.  Da yake yanke hukunci, kwamitin mutum uku ya ce kotun ta yi kuskure wajen yanke hukuncin cewa Gwamna Sule bai samu rinjayen kuri’un da aka kada a zaben ba.  Cikakken labarin zai zo muku nan gaba