Search This Blog

Showing posts with label Tallafin azumi. Show all posts
Showing posts with label Tallafin azumi. Show all posts

Wednesday, 5 March 2025

Abdulmumin Kofa ya raba gagarumin tallafin azumi ga mutum 10,000 a Kiru da Bebeji


Kamar yadda ya saba, Mai Girma Dan Majalisar Wakilai na mazaɓar Kiru/Bebeji, Kano, Hon. Abdulmumin Jibrin Kofa PhD (Jarman Bebeji), ya raba tallafi ga al’ummar yankinsa domin rage musu radadin rayuwa, musamman a watan azumin Ramadan. 

A wannan karon, Mai Girma Hon. Kofa ya raba tallafin kudade ga mata da maza har mutum dubu goma.

Daga ciki akwai waɗanda suka samu tallafin ₦200,000, da masu ₦100,000, da masu ₦50,000, sai masu ₦20,000 da kuma masu ₦10,000. 

Baya ga haka, matasa dubu biyu sun samu damar cin gajiyar shirin tallafin rabon kayan sana’a da zai taimaka musu wajen dogaro da kawunansu

Allah ya sada mu da alkhairan da ke cikin wannan watan na Ramadan mai albarka. Amin.


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...