Search This Blog

Showing posts with label Zaben Gwamnan Kano. Show all posts
Showing posts with label Zaben Gwamnan Kano. Show all posts

Friday, 12 January 2024

GAME DA SHARI’AR ZABEN JIHAR KANO: ABINDA YAI SAURA - Saidu Ahmad Dukawa

Bismillahir Rahmanir Raheem
Yau, Juma’a 12/1/2024, Allah ya kawo karshen dakon da aka sha wajen sanin wanene halartaccen Gwamna a Jihar Kano. 

Ina zaton an dade al’umar Kano, da wadanda suka damu da halin da Kano take ciki a fadin Duniya, ba su shiga zulumi (tension) da fargaba (anxiety) kamar a wadannan watannin da aka gudanar da shari’u a mataki daban daban ba. Alhamdu lillah, Allah ya nunawa wadanda suke raye karshen dambarwar. Muna fatan kada Allah ya sake jarrabar Bayinsa da irin wannan halin.

Yanzu abu uku ne suka saurar mana. Abu na farko shine kowa ya karbi hukuncin da zuciya daya. Wandanda suka yi nasara kada su dauka iyawarsu ce, wadanda ba su samu yadda suke so ba kada su dauka wani ne ya janyo musu. Wannan ne zai taimaka wajen kaucewa irin wannan jarrabawar anan gaba.

Abu na biyu shine gawmanati da dukufa wajen samar da shugabanci nagari, ba tare da tunanin ramuwar gayya ba, ko wariya, ko wani abu mai kama da haka. Ya kamata a sani cewar gwargwadon yadda al’umma take da hadin kai gwargwadon yadda shugabanci zai yi sauki ya yi inganci. 

Abu na karshe shine yana da kyau ‘Yansiyasa su taimaki kansu da sauran al’umma su ragewa mutane shari’un zabe. Idan za a iya tunawa su kan hadu su saka hannu na alkawarin ba za su janyo tashin hankaili ba wajen yin zabe. To su kara da wasu alkawuran guda hudu, kamar haka:

1. Ba za su yi duk wani nau’i na magudi ba a harkar zabe

2. Ba za su yi amfani da ‘Yan Daba ba wajen tsorata mutane zuwa wajen zabe

3. Duk wanda aka ce ya fadi zabe ba zai je kotu neman a yi musu shari’a da wanda ya ci zabe ba; sannan

4. Wanda ya ci zabe ba zai tozarta wanda ya fadi ba, ta kowace hanya.

Ina kyautata zaton idan aka yi haka za a daina shari’un zabe, zai zama al’umma ne alkalai na koli a harkar zabe, kuma za su rika yanke hukunci ne a gindin akwatin zabe.

Amman fa na san fadar daban, aikatuwar daban. Don babu mamaki idan mafarki kawai nake yi.

Ko ma dai menene, Allah ya sa mu dace da shugabanci nagari.


Monday, 18 December 2023

Kotun Koli Ta Tsayar Da Ranar Da Za Ta Saurari Karar Zaben Gwamnan Kano

Kotun koli ta sanya ranar Alhamis 21 ga watan Disamba domin cigaba da sauraron karar zaben gwamnan Kano tsakanin gwamna Abba Kabiru Yusuf na jam’iyyar New Nigeria Peoples Party NNPP da Nasiru Yusuf Gawuna na jam’iyyar APC. 

KANO FOCUS ta rawaito cewa a cikin sanarwar da magatakardar kotun daukaka kara ta aikewa lauyoyin bangarorin biyu, kotun za ta saurari karar da NNPP ta shigar da kararrakin wasu jam’iyyu. 

Gwamna Yusuf na kalubalantar hukuncin da wasu bangarori uku na kotun daukaka kara suka yanke wanda ya soke nasarar da ya samu tare da tabbatar da hukuncin da kotun sauraren kararrakin zabe ta yanke. Kotun sauraron kararrakin zabe karkashin jagorancin mai shari’a Osedebay ta bayyana dan takarar jam’iyyar APC, Nasiru Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Kano a watan Maris. 

Kotun daukaka kara ta yi watsi da karar da Gwamna Yusuf ya shigar bisa matsayinsa na zama mamba a jam’iyyarsa sannan ta zargi kotun da yin watsi da hujjar da ta yanke. Kotun ta kori Gwamna Yusuf ne saboda amfani da takardun zabe da hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ba ta sa hannu, ko kwanan wata ko tambari ba. 

An dai samu rudani a dukkan shari'ar yayin da NNPP ta gano hujjojin da CTC na kotun daukaka kara da ta tabbatar da Gwamna Yusuf a matsayin wanda ya lashe zaben, wanda ya sabawa abin da alkalan kotun suka karanta. Raba wannan: 
 

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...