Posts

Showing posts with the label Pakistan

Shugaba Tinubu Ya Nada Farfesa Pakistan A Matsayin Shugaban Hukumar NAHCON

Image
Shugaba Bola Tinubu ya nada Farfesa Abdullahi Saleh Usman  a matsayin sabon shugaban hukumar alhazai ta kasa (NAHCON), inda ya sauke shugaban da ya gabata, Jalal Arabi, bisa zargin cin hanci da rashawa.  Farfesa Pakistan fitaccen malami ne da ya yi digirinsa na farko a Jami’ar Madina da Jami’ar Peshawar da ke Pakistan.  A baya ya taba rike mukamin Shugaban Hukumar Alhazai ta Jihar Kano, inda ya samu nasarar kula da ayyukan mafi yawan alhazan kasar nan.   A cewar wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban kasar Ajuri Ngalale ya fitar, majalisar dattawa ta tabbatar da nadin. “Shugaban kasa yana sa ran sabon shugaban NAHCON ya yi aikinsa bisa gaskiya, da rikon amana ga kasa,” in ji sanarwar.  Wannan ci gaban dai na zuwa ne bayan da Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arziki Tu’annati (EFCC) ta gurfanar da tsohon Shugaban Hukumar, Jalal Arabi, da Sakataren Hukumar, Abdullahi Kontagora bisa zargin karkatar da wasu sassan N90bn da Gwamnatin Tarayya ta fitar don tallafawa shekarar aikin hajin na

Labari Da Dumiduminsa: Tawagar Farko Ta Maniyyatan Kasar Pakistan Mai Dauke Da Mutum 138 Sun Sauka A Makkah

Image
Kashi na farko na jigilar alhazan Pakistan ya isa Makkah domin kammala shirye-shiryen mahajjatan Pakistan. Wakilin Rediyon Pakistan Javed Iqbal ya ruwaito daga Makkah cewa rukunin mutane 138 sun hada da Moavineen 19, kwararrun likitoci 67 da kuma jami’an ma’aikata 52 na ma’aikatar kula da harkokin addini. Tawagar za ta kafa sansanonin kula da lafiya tare da kammala wasu shirye-shirye da suka hada da wurin kwana, sufuri da kuma wuraren cin abinci ga alhazan Pakistan. Yana da kyau a ambaci cewa aikin jigilar alhazai na Pakistan zai fara aiki daga gobe. Bayan shekarar 2019, wannan shi ne aikin Hajji na farko mai cikakken karfi wanda a karkashinsa kimanin alhazan Pakistan 180,000 ne za su tafi kasar Saudiyya don sauke farali. A bisa umarnin na musamman na ministan harkokin addini Talha Mahmood, ma'aikatan ma'aikatar suna yin kokari sosai don ganin aikin Hajjin bana ya samu nasara.

Firaministan Pakistan ya tsallake rijiya da baya

Image
  Firaministan Pakistan Shehbaz Sharif ya tsallake rijiya da baya, bayan da ‘yan majalisar kasar suka kada kuri’ar yanke kauna, yayin da sauran kungiyoyin fararen hula suka matsa kan a fara shirin gudanar da babban zaben kasar.  Sharif ya sami kuri’un amincewa guda 180, yayin da ‘yan majalisa 172 suka nuna rashin amincewa da salon shugabancin sa, abinda ya bashi damar ci gaba da rike mukamin sa da kyar.  Ko da yake jawabi, kakakin majalisar dokokin kasar Raja Pervais Asharf, yace a yanzu abinda majalisar zata mayar da hankakli shine batun babban zaben da ke tafe.  Sharif wanda ya gaji Imran Khan ya yabawa mambobin jam’iyyyar sa da ke majalisar bayan da suka amince da salón mulkin sa, tare da yanke hukuncin sake bashi dama, ta hanyar kada kuri’ar amincewa da shi.  rfi