Posts

Showing posts with the label Masarautar Dutse

Yanzu-Yanzu: Gwamnan Jigawa ya amince da nadin Sabon Sarkin Dutse

Image
Gwamnan jihar Jigawa Muhammad Badaru Abubakar ya amince da nadin Muhammad Hameem Nuhu Sanusi a matsayin sabon sarkin Dutse. Kadaura24 ta rawaito Sanarwar amincewa da nadin na dauke da sa hannun kwamishinan aiyukan na musamman na jihar Jigawa Auwalu D Sankara,wadda kuma aka rabawa manema labarai. Nadin ya biyo bayan zaben Masu Zaben Sarki na Masarautar Dutse su bakwai suka yi wa Hameem daga cikin masu neman kujerar sarautar har su su uku.  Majalisar Sarakunan Jihar Jigawa ta amince da zaben, sannan kuma nadin sa ya fara aiki daga ranar 5 ga Fabrairu, 2023.  Sabon Sarkin dai ya gaji Mahaifinsa ne Alhaji Nuhu Muhd Sanusi II wanda Allah ya yiwa rasuwa a makon daya