Posts

Showing posts with the label Kasar Waje

Najeriya Za Ta Fara Fitar Da Tataccen Mai Kasar Waje A 2024 —NNPCL

Image
Shugaban Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) Mele Kyari ya ce Najeriya za ta zama kasa mai fitar da tataccen man fetur da dangoginsa zuwa kasashen waje a shekarar 2024 mai kamawa. Mele Kyari ya kuma ba wa ’yan Najeriya tabbacin cewa cikin watanni uku masu zuwa ba za a samu karancin man fetur ba, kamar yadda ake gani a lokacin bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara. “Ina tabbatar wa shugabannin majalisa ba za a fuskanci karancin mai ba. “Za ku ji ana ta yada labarin layuka a gidajen mai, amma ba gaskiya ba ne,” in ji Mele Kyari. Hukuncin da muka zartar na korar Gwamnan Kano na nan daram – Kotu Magoya bayan NNPP sun yi zanga-zanga kan hukuncin kotu a Kano Ya bayyana hakan ne lokacin da ya ziyarci shugabannin majalisar dattawa. Ya kara da cewa NNPC zai gyara matatar mai ta garin Fatakwal a wata mai kamawa, sannnan matatar mai ta Warri ta biyo baya a farkon 2024. Haka zalika, ya yi hasashen NNPCL zai samu ribar da ta kai triliyan biyu a shekarar 2023 da ke dab da karewa. Kyari ya shai

Ba Ni Da Gida A Kasar Waje - Buhari

Image
Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya ce ba shi da gida a wajen Najeriya. Ya bayyana haka ne a lokacin da yake karbar wasikar girmamawa daga jakadan Birtaniya a Najeriya, Richard Hugh Montgomery da takwaransa na Sri Lanka Velupillai Kananathan a fadar shugaban kasa a ranar Alhamis. Buhari ya ce “A daya daga cikin ganawarmu da Sarki Charles III, ya tambaye ni ko ina da gida a Ingila, amma na shaida masa cewar ba ni da gida a wajen Najeriya.” Ya kara da cewa, an shafe shekaru da yawa ana musayar al’adu ta hanyar ilimi da horarwa tare da Birtaniya, inda ya nuna cewa ya samu horon soji a makarantar Mons Officer Cadet da ke Aldershot a Ingila 1962 zuwa 1963. Buhari ya shaida wa jami’in diflomasiyyar Birtaniya cewa kyakkyawar fahimtar banbance-banbancen al’adu, da mutunta cibiyoyi shi ne ya share fagen yawan nasarorin da Birtaniya ta samu. Ya ce jami’an diflomasiyyar da suka gabata sun kulla alaka da Sarkin Musulmi, Sarkin Kano, Shehun Borno da Sarkin Ilorin. Shugaba Buhari ya kuma

Abun Da Tinibu Da Kwankwaso Suka Tattauna A Kasar Waje

Image
Shugaban kasa mai jiran gado, Bola Tinubu ya yi wata ganawar sirri da dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Kwankwaso a kasar Faransa. Wata majiya mai tushe ta ce Tinubu ya yi wa Kwankwaso tayin tafiya tare da shi a sabuwar gwamnati da kuma duba yiwuwar sulhu tsakaninsa da Gwamnan Kano mai barin gado, Abdullahi Ganduje. A ranar Litinin, mako biyu kafin Tinubu ya karbi rantsuwar fara aiki, suka shafe sama da awa hudu suna ganawar sirrin da Kwankwaso a birnin Paris na kasar Faransa. Majiyarmu ta ce a yayin ganawar, Tinubu ya bukaci hadin kai domin aiki tare da Sanata Kwankwaso — wanda ya lashe kuri’un Jihar Kano a zaben 2023. Kwankwaso da shugaban kasar da ke jiran rantsarwa nan da mako biyu masu zuwa sun kuma amince za su ci gaba da tattaunawa kan wannan batu. Majiyar ta ce mai dakin Kwankwaso da zababben Sanata Abdulmumini na Jam’iyyar NNPP ne suka raka madugun Kwankwasiyya zuwa wurin ganawar. A bangaren Tinubu kuma, matarsa, Sanata Oluremi da Mataimakin