Search This Blog

Showing posts with label Kasar Waje. Show all posts
Showing posts with label Kasar Waje. Show all posts

Thursday, 23 November 2023

Najeriya Za Ta Fara Fitar Da Tataccen Mai Kasar Waje A 2024 —NNPCL

Shugaban Kamfanin Mai na Kasa (NNPCL) Mele Kyari ya ce Najeriya za ta zama kasa mai fitar da tataccen man fetur da dangoginsa zuwa kasashen waje a shekarar 2024 mai kamawa.

Mele Kyari ya kuma ba wa ’yan Najeriya tabbacin cewa cikin watanni uku masu zuwa ba za a samu karancin man fetur ba, kamar yadda ake gani a lokacin bukukuwan Kirsimeti da Sabuwar Shekara.

“Ina tabbatar wa shugabannin majalisa ba za a fuskanci karancin mai ba.


“Za ku ji ana ta yada labarin layuka a gidajen mai, amma ba gaskiya ba ne,” in ji Mele Kyari.


Hukuncin da muka zartar na korar Gwamnan Kano na nan daram – Kotu
Magoya bayan NNPP sun yi zanga-zanga kan hukuncin kotu a Kano
Ya bayyana hakan ne lokacin da ya ziyarci shugabannin majalisar dattawa.

Ya kara da cewa NNPC zai gyara matatar mai ta garin Fatakwal a wata mai kamawa, sannnan matatar mai ta Warri ta biyo baya a farkon 2024.

Haka zalika, ya yi hasashen NNPCL zai samu ribar da ta kai triliyan biyu a shekarar 2023 da ke dab da karewa.

Kyari ya shaida wa shugabannin majalisar dattawa cewa amincewa da sabuwar dokar man fetur, ta saka man ya wadata kuma a farashi mai sauki a kasar nan.


Da yake jawabi kan matsalar fasa bututu da satar mai, Kyari ya ce jami’an tsaro na musamman da ke yaki da bata-garin, sun taimaka musu wajen kwato gangunan danyen mai na kusan naira miliyan biyu.

Da yake jawabi, shugaban majalisar dattawa, Godswill Akpabio, ya gode wa kamfanin man bisa hadin kai da ya bai wa Gwamnatin Tarayya wajen cire tallafin man fetur.

(AMINIYA)

Thursday, 18 May 2023

Ba Ni Da Gida A Kasar Waje - Buhari

Shugaban kasa Muhammadu Buhari, ya ce ba shi da gida a wajen Najeriya.

Ya bayyana haka ne a lokacin da yake karbar wasikar girmamawa daga jakadan Birtaniya a Najeriya, Richard Hugh Montgomery da takwaransa na Sri Lanka Velupillai Kananathan a fadar shugaban kasa a ranar Alhamis.

Buhari ya ce “A daya daga cikin ganawarmu da Sarki Charles III, ya tambaye ni ko ina da gida a Ingila, amma na shaida masa cewar ba ni da gida a wajen Najeriya.”

Ya kara da cewa, an shafe shekaru da yawa ana musayar al’adu ta hanyar ilimi da horarwa tare da Birtaniya, inda ya nuna cewa ya samu horon soji a makarantar Mons Officer Cadet da ke Aldershot a Ingila 1962 zuwa 1963.

Buhari ya shaida wa jami’in diflomasiyyar Birtaniya cewa kyakkyawar fahimtar banbance-banbancen al’adu, da mutunta cibiyoyi shi ne ya share fagen yawan nasarorin da Birtaniya ta samu.

Ya ce jami’an diflomasiyyar da suka gabata sun kulla alaka da Sarkin Musulmi, Sarkin Kano, Shehun Borno da Sarkin Ilorin.


Shugaba Buhari ya kuma umarci Montgomery da ya ci gaba da kiyaye kyawawan manufofin diflomasiyya, kamar yadda magabata suka yi, ta hanyar mutunta cibiyoyin gargajiya a Najeriya.

Ya ce dangantakar da ke tsakanin Birtaniya da Sri Lanka za ta kara inganta tare da la’akari da al’adun gida, sarakunan gargajiya, da sauransu.

“Ina jin dadin yadda ake girmama sarakunanmu da hukumominmu, duk da sauyin zamani, ilimi, da karuwar son abin duniya.

“Akwai abubuwa da yawa da za mu koya daga al’adunmu, kuma cibiyoyin gargajiya su ne masu kula da su, kuma ya kamata kowa ya mutunta su,” in ji Buhari.

Ya shaida wa jakadan Birtaniya cewa, huldar diflomasiyyar da ta shafe shekaru da dama tana ci gaba da dorewa bisa mutunta al’adu za ta kara karfi.

A nasa bangaren, Montgomery, ya ce Birtaniya a kodayaushe tana girmama Najeriya da al’adunta, yayin da ya bayyana fatan alheri ga Sarki Charles III, a daidai lokacin da Najeriya ke shirin mika mulki a ranar 29 ga watan Mayun 2023.

Shi ma a nasa jawabin, jakadan Sri Lanka ya shaida wa shugaba Buhari cewa kasar za ta ci gaba da bai wa sojojin Najeriya kwarewa da gogewa wajen yaki da ta’addanci.
AMINIYA 

Tuesday, 16 May 2023

Abun Da Tinibu Da Kwankwaso Suka Tattauna A Kasar Waje


Shugaban kasa mai jiran gado, Bola Tinubu ya yi wata ganawar sirri da dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar NNPP, Sanata Rabiu Kwankwaso a kasar Faransa.

Wata majiya mai tushe ta ce Tinubu ya yi wa Kwankwaso tayin tafiya tare da shi a sabuwar gwamnati da kuma duba yiwuwar sulhu tsakaninsa da Gwamnan Kano mai barin gado, Abdullahi Ganduje.

A ranar Litinin, mako biyu kafin Tinubu ya karbi rantsuwar fara aiki, suka shafe sama da awa hudu suna ganawar sirrin da Kwankwaso a birnin Paris na kasar Faransa.

Majiyarmu ta ce a yayin ganawar, Tinubu ya bukaci hadin kai domin aiki tare da Sanata Kwankwaso — wanda ya lashe kuri’un Jihar Kano a zaben 2023.
Kwankwaso da shugaban kasar da ke jiran rantsarwa nan da mako biyu masu zuwa sun kuma amince za su ci gaba da tattaunawa kan wannan batu.

Majiyar ta ce mai dakin Kwankwaso da zababben Sanata Abdulmumini na Jam’iyyar NNPP ne suka raka madugun Kwankwasiyya zuwa wurin ganawar.

A bangaren Tinubu kuma, matarsa, Sanata Oluremi da Mataimakin Shugaban Majalisar Wakilai mai barin gado, Femi Gbajabiamila, ne suka raka shi.

Majiyar ta ce “Matar Tinubu, Sanata Oluremi ce ta karbi bakuncin Hajiya Hafsa, a yayin da ‘yan siyasar kuma suka dauki tsawon lokaci suna tattauna a kan hadin kan kasa da abubuwan da sabuwar gwamnati za ta ba wa muhimmanci.

“Sauran sun hada da batun shugabancin Majalisar Dokoki ta Kasa da kuma aniyar zababben shugaban kasan na kafa gwamnatin hadin kan kasa da ake fatan damawa da Kwankwaso a ciki.

“Sun kuma yi waiwaye a kan kawancensu na siyasa tun suna lokacin da suke Majalisar Dokoki ta Kasa a shekarar 19992,” in ji majiyar.

Majiyar ta kara da cewa a yayin zaman an kuma fara tunanin sasanta tsakanin Kwankwaso da tsohon mataimakinsa, wato Gwamnan Kano mai barin gado, Abdullahi Ganduje.

A shekarar 2015 Ganduje ya gaji kujerar Kwankwaso, amma ba da jima ba daga baya suka raba gari, kuma har yanzu ba sa ga-maciji.
AMINIYA 

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

SAPZ Kano partners ABCOAD to organize FFS Training for Youth and Women.

The Special Agro-Industrial Processing Zones (SAPZ) Programme, Kano State, in collaboration with Audu Bako College of Agricultur...