Kuyi amfani da kalaman da al'uma zasu gamu dasu wajan yakin neman zabe: Mai Martaba Sarkin Kano.

Mai martaba sarkin kano Alhaji Aminu Ad Bayero ya yi kira ga masu neman kujerun mulkin kasar nan da su tabbatar sunyi kalamai da al'umma za su gamsu da su wajen neman kuri'ar alumma a zaben shekarar 2023.

A sanarwar da Sakataren yada labaran Masarautar Abubakar Balarabe Kofar Naisa ya sanyawa hannu, ta ce Sarkin ya bayyana haka ne lokaci da dan takarar shugaban kasa na jam'iyar SDP Adewale Adebayo da dantakar kujerar gwamnan jihar Kano Dr. Muhammad Bala gwagwarwa yayin da su ka  ziyar ce shi a fadar sa.

Alhaji Aminu Bayero, ya kuma nemi da duk wani dake neman kujerar da yasan cewa Allah ne ke bayar da Mulki bawai karfin ikon tada zaune tsayeba.

Da yake nasa jawabin, dan takarar Gwamna na jam'iyyar ta SDP Bala Muhammad Gwagwarwa ya ce sun ziyarci fadar sarkin ne domin neman tabaraki da addu'ar.

A wani cigaban kuma Martaba Sarkin kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya nada Dr. Malam Umar Ibrahim Indabawa  a matsayin sabon limamin  Masallacin Darul hadis dake Unguwar Tudun Yola a Karamar  Hukumar Gwale.


Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki