Posts

Showing posts with the label Eid-El-Fitr

Eid-El-Fitr: Gwamna Yusuf ya taya al'ummar Musulmi murna

Image
Gwamnan Jihar Kano Alhaji Abba Yusuf ya mika sakon taya murna ga al’ummar Musulmi da sauran al’ummar Kano bisa samun nasarar kammala azumin watan Ramadan, tare da taya su murnar zagayowar ranar Sallah. A wata sanarwa da mai magana da yawunsa, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, gwamnan ya jaddada muhimmancin kiyaye kyawawan halaye na tausayi, karamci, da'a, kishin kasa, da zaman tare da juna da aka sanya a cikin watan Ramadan. “Yayin da watan Ramadan ya zo karshe, kuma aka ga jinjirin watan Shawwal, ka’idojin tausayi, karamci, horo, kishin kasa, da zaman lafiya da ya sanya ya kamata kowa da kowa ya rungumi shi domin ci gaban al’ummar da muke fata baki daya”. Ya bukaci al’ummar Kano masu girma da su rika rokon Allah ya basu jagoranci a dukkan bangarori. Gwamna Yusuf ya yi wa al’ummar Kano alkawarin cewa gwamnatinsa za ta samar da ingantattun tsare-tsare don samar da zaman lafiya da hadin kai ga kowa da kowa. “Kwanakun alÆ™awarin suna jiran al’ummar Kano saboda gwamnati m