Posts

Showing posts with the label rikicin Sudan

Mu Tashi Tsaye Domin Kawo Karshen Rikicin Sudan — Aisha Buhari

Image
Uwargidan Shugaban Najeriya, Aisha Buhari ta roki a hada karfi da karfe don ganin kurar rikicin Sudan ta kwanta. Jaridar Premium Times ta ruwaito Aisha Buhari na wannan kira a wani taro da ta jagoranta jiya Litinin a Fadar Gwamnati da ke Abuja. A cewar jaridar, Aisha Buhari na ganin akwai rawar da matan shugabannin Afirka za su iya takawa musamman wajen kai agaji Sudan. Sama da mutane 500 ake kyautata zaton cewa rikicin ya yi sanadin rasuwarsu kawo yanzu. Mutum sama 700,000 sun rasa muhallansu Alkaluman mutanen da rikicin Sudan ya raba da muhallansu ya ninka zuwa sama da mutum 700, 000, a cewar Majalisar Dinkin Duniya. Karuwar mutanen da ke guje wa muhallansu ya sanya fargaba kan yaduwar fadan duk da tattaunawar tsagauta bude wuta da ake yi a Saudiyya. Khartoum na da al’umma kusan miliyan 5.4, sai dai an daidaita birnin mai cike da zaman lafiya a baya tun bayan barkewar fada a ranar 15 ga watan Afrilu. Tun ranar 15 ga watan Afrilu, yaki ya barke a Sudan kuma har wannan loka

HAJJIN 2023: Rikicin Sudan Ka Iya Kawo Matsala Ga Jigilar Ahazan Najeriya - Kungiyar Fararen Hula

Image
Rikicin da ake fama da shi a kasar Sudan na iya kawo cikas ga jigilar maniyyatan Najeriya zuwa kasar Saudiyya cikin sauki, domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2023, in ji kungiyar daukar rahotannin aikin hajji mai zaman kanta.   Kungiyar farar hula a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Juma'a mai dauke da sa hannun shugabanta na kasa Ibrahim Muhammad, ta ce tuni yakin ya kai ga rufe sararin samaniyar Sudan ba zato ba tsammani.   Kungiyar ta ce Najeriya "dole ne ta hanyar NAHCON ta yi gaggawar sake duba kalubalen da ke gabanta sannan ta fito da wasu zabin da za a yi a matsayin ma'auni."   Kamar yadda jadawalin NAHCON ya nuna, za a fara jigilar maniyyatan Najeriya zuwa kasa mai tsarki a ranar 21 ga Mayu, 2023.   Jiragen saman jigilar alhazan Najeriya na tafiya ta sararin samaniyar Sudan a lokacin da suke tafiya Saudiyya, kuma ana daukar matsakaicin sa'o'i hudu zuwa biyar kafin su isa kasar.   Sai dai kuma rufe sararin samaniyar kasar Sudan ba z

Air Peace Zai Kwaso Daliban Najeriya Da Suka Makale A Sudan Kyauta

Image
  Kamfanin jiragen sama na Air Peace ya ce zai kwaso daliban Najeriya da suka makale a kasar Sudan inda yaki ya barke, kyauta zuwa gida. Rikicin shugabanci ya kazance a Sudan a baya-bayan nan, har ta kai ga rufe sararin samaniyar kasar. Akalla daliban Najeriya 5,000 da ke Sudan sun nuna matukar bukatar a dawo da su gida, inda wasu daga cikinsu ke kokarin tsallaka iyaka zuwa kasar Habasha, mai makwabtaka da Sudan. Shugaban kamfanin Ake Peace, llen Onyema, ya sanar da cewa idan ’yan Najeriya da ke Sudan za su iya tsallaka iyaka zuwa kasashen makwabtakan Sudan, to kamfaninsa zai kwaso su zuwa gida a kyauta. Ya ce aikin kwaso su ya wuce a bar wa gwamnati ita kadai, saboda bai kamata a yi asarar dan Najeriya ko daya ba a rikicin na Sudan. Gwamnatin Tarayya dai ta yi alkawarin ranar Talata za ta fara kwaso ’yan Najeriyan ta kasar Habasha. Wata sanarwa da Fadar Shugaban Kasa ta fitar ta ce Ma’aikatarta Harkokin Kasashen Waje na aiki da gwamantin kasar Habasha, domin amfani da sara