Search This Blog

Showing posts with label Peter Obi. Show all posts
Showing posts with label Peter Obi. Show all posts

Tuesday, 5 March 2024

Matukin Adaidaita Sahu Dan Kano Da Ya Tsinci Kudi Ya Mayar, Ya Samu Tallafin Miliyan 250 Don Yin Karatu

A wani abin da ya yi kama da gasa, matashin nan mai tuka Adaidaita Sahu mai shekaru 23 a Kano, Auwalu Salisu, wanda ya tsinci kudin wani dan kasuwa dan kasar Chadi har naira Miliyan 15  da ya manta su a kekensa tun a 2023, an ba shi tallafin karatu na naira Miliyan 250 har zuwa matakin karatun digiri na uku 

KANO FOCUS ta ruwaito cewa, LEADERSHIP Media Group ta yi bikin karamar  Auwalu a ranar Talata a wajen taron shekara-shekara da kuma bikin karramawa a matsayin wanda ya lashe lambar yabo ta ‘Fitaccen matashin matashin shekarar 2023’, saboda nuna gaskiya da ya yi.

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar Labour Party (LP), Peter Obi, wanda aka karrama shi a matsayin Gwarzon dan siyasar LEADERSHIP na shekarar 2023, shi ne ya fara ba Awwalu guraben karatu a Jami’ar Baze da ke Abuja har zuwa matakin digirin digirgir.


Bayan haka, gwamnan jihar Neja, kuma wanda ya lashe kyautar Gwarzon Gwamnan na LEADERSHIP, Mohammed Umar Bago, ya mayar da martani cikin raha yana mai cewa jam’iyyar Labour ba za ta iya zarce jam’iyyar APC mai mulki ba.

A sakamakon haka Bago ya sanar da kyautar N250m ga Awwalu don jin dadin aikinsa na gaskiya da kuma karfafawa sauran matasan Najeriya kwarin gwiwa don nuna halin kirki.

Ya ce Awwalu zai samu tallafin Naira miliyan 50 kowanne daga gare shi da kansa da kuma shugaban kasa Bola Tinubu da ministocinsa da kungiyar gwamnonin APC da kuma gwamnatin jihar Neja.


Bago ya kara da cewa zai bayyana daya daga cikin ayyukan tituna da yake gudanarwa a jihar Neja da sunan matukin babur din na Kano.

Wednesday, 12 April 2023

Yadda jami'an tsaro suka tsare Peter Obi a London

 


Kwamitin yaƙin neman zaɓen shugaban ƙasa na jam’iyyar LP ya ce jami’ai sun tsare tare da hantarar ɗan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyar, Peter Obi a birnin London.

Mai magana da yawun kwamitin kamfe na jam’iyyar LP, Diran Onifade ne ya bayyana haka a cikin wata sanarwar da ya fitar a ranar Laraba.

Sanarwar ta ce lamarin ya faru ne a filin jirgin sama na Heathrow da ke London.

Ta ƙara da cewa jami’an shige da fice na Birtaniya ɗin ne suka titsiye tsohon ɗan takarar shugaban ƙasar.

Diran Onafide ya ce hukumomi a Birtaniya sun tsare tare da yin tambayoyi ga tsohon gwamnan na jihar Anambra kan wani lamari da ya shafi wani mutum da ke yin sojan-gona da suna Peter Obi.

Sanarwar ta ƙara da cewa jami’an sun sassauta wa Petetr Obi ne bayan wasu ƴan Najeriya da ke a filin jirgin sun sanya baki.

Peter Obi dai ya isa birnin na London ne domin bukukuwan Easter na mabiya addinin Kirista.

Bayanin ya nuna cewa bayan saukar Peter Obi a filin jirgin na Heathrow da ke London, jami’an tsaro sun zo wurin sa a lokacin da yake kan layin tantancewa, tare da miƙa masa wata takarda da ke ƙunshe da umurnin tsarewa, sannan suka buƙace shi da ya fita daga layi.

Onifande ya ce jami’an sun yi wa Peter Obi tambayoyi na tsawon lokaci, wanda abu ne da ba a saba ganin ya faru ga wani mutum da ya kwashe sama da shekara 10 yana rayuwa a ƙasar ba.

Sai dai mutane ƴan asalin Najeriya sun rinƙa ɗaga muryoyinsu domin sanin dalilin da ya sa aka tsare tsohon gwamnan.

Me ya sa aka tsare Obi?

Matakin da ƴan Najeriya suka ɗauka na tambayar dalilin da ya sa aka tsare Peter Obi a filin jirgin ya tursasa wa jami’an shige da ficen yin bayani kan musabbabin tsare shi.

Sun ce suna masa tambayoyi ne kan wani abu da ya jiɓanci sojan-gona.

Onifade ya ce illar sojan-gona ita ce akwai yiwuwar wanda ke sojan-gonar zai iya aikata laifukan da za a maƙala wa shi Peter Obi.

BBC

Tuesday, 4 April 2023

Gwamnatin Najeriya Na Zargin Peter Obi Da Cin Amanar Kasa

 


Gwamnatin Tarayya ta shawarci dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar LP a zaben da ya gabata, Peter Obi, da ya guji tunzura jama’a su tayar da zaune tsaye kan sakamakon zaben da ya gabata.

Ministan Yada Labarai da Al’adu, Alhaji Lai Mohammed ne ya bayar da shawarar yayin wata tattaunawarsa da kafafen yada labarai a birnin Washington DC na Amurka.

Kamfanin Dillancin Labarai na Najeriya (NAN) ya rawaito cewa Ministan ya je Amurka ne don tattaunawa da kafofin kan abubuwan da suka wakana yayin zaben da ya gabata a Najeriya.

NAN ya ce ya zuwa yanzu, Ministan ya tattauna da jaridar Washington Post da Muryar Amurka da mujallar Foreign Policy da kuma kamfanin dillancin labarai na AP.

Lai Mohammed ya kuma gargadi Peter Obi da cewa ba daidai ba ne ya rika neman hakkinsa a kotu, sannan kuma ya rika kokarin tayar da zaune tsaye a daya bangaren.

“Obi da Mataimakinsa Datti, bai kamata su rika yi wa zababben Shugaban Najeriya, Bola Tinubu na APC barazana cewa muddin aka rantsar da shi ranar 29 ga watan Mayu mai zuwa, Dimokuradiyya ta kare a Najeriya.

“Wannan cin amanar kasa ne. Neman tayar da zaune tsaye ne. Kuma abin da suke kokarin yi ke nan.

“Kalaman Obi dan ko a mutu ko a yi rai ne, bai mai son Dimokuradiyyar da yake ikirari ba ne shi, saboda mai sonta bai kamata ya yi amanna da ita kawai lokacin da ya lashe zabe ba,” in ji Ministan.

Monday, 9 January 2023

Zan tattauna da masu tayar da kayar baya idan na zama shugaban kasa - Peter Obi

Ɗan takarar gwamna a Jam'iyyar Labour a Najeriya Peter Obi ya ce zai buƙaci ya tattauna da duk wani ɗan gwagwarmaya ko kuma masu tayar da ƙayar baya da gwamnatin Najeriya ta ɗaure idan ya samu mulkin ƙasar.

Mista Obi ya bayyana haka ne a wani zauren tattaunawa da tambayoyi da gidan talabijin na Channels a Najeriya ya shirya ga ɗan takarar da mataimakinsa.

Ko da wani ya tambayi Mista Obi ko cikin waɗanda zai tattauna da su har da ƴan Boko Haram da ke jawo matsaloli a arewacin Najeriya da kuma ƴan ƙungiyar IPOB da ke kudu maso gabashin ƙasar, sai ya ce " Zan tattauna da dukansu, ko ma wace irin bindiga ce suke ɗauke da ita".

Mista Obi ya ce ko da mutum yana ɗaure a gidan yari ne zai je ya fito da shi domin su zauna su tattauna.


Mista Obi ya ce ya yanke hukuncin yin haka ne domin ganin cewa an samu zaman lafiya a ƙasar.

"Zan tattauna da waɗanda suke so a tattauna da su. Sai an kalli me ke jawo suke gwagwarmaya; batu ne na rashin adalci ko lamari ne na talauci ko rashin aikin yi," in ji Mista Obi.

Mista Obi ya bayyana cewa idan gwamnati ta soma mayar da hankali kan batun zama da tattaunawa da ƴan ƙasar, babu wani ɗan gwagwarmaya a duniya da zai samu wani dalili na tayar da zaune tsaye sakamakon duk wata buƙata an biya ta.

Najeriya dai ta sha fama da zanga-zanga ta masu son ɓallewa daga ƙasar kamar ƙungiyar IPOB masu iƙirarin kafa ƙasar Biafra.

Yanzu haka jagoran ƙungiyar Nnamdi Kanu na ci gaba da zama a tsare a hannun jami'an tsaron Najeriya kan wasu zarge-zarge ciki har da na ta'addanci
(BBC HAUSA) 

Sunday, 1 January 2023

2023: Peter Obi Ne Dan Takarata —Obansajo

 


A karon farko tsohon shugaban kasa, Olusegun Obasanjo, ya fito bainar jama’a ya bayyana goyon bayansa ga dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar LP, Peter Obi, a zaben 2023.

Da yake bayyana goyo bayan nasa a cikin sakonsa na murnar shiga Sabuwar Shekarar 2023, Obasanjo ya ce Peter Obi ya yi wa sauran ’yan takarar shugaban kasa fintinkau wajen  ilimi da kwarewa.

  • https://noordakata.blogspot.com/2023/01/abdulmumin-jibrin-kofa-ya-raba-tallafin.html
  • https://noordakata.blogspot.com/2023/01/gwamnan-jihar-kano-abdullahi-umar.html

A cikin sakonsa nasa mai mai taken, “Rokona ga ’yan Najeriya, musamman matasa,” Obasanjo ya ce, “Duk da cewa a cikin masu masu takarar babu wani shafaffe da mai, amma a cikin Peter Obi ya fi sauran nagarta ta bangaren kyawun dabi’u, gogewa, fahimta, abin da suka yi a baya da wanda za su iya kawowa.”

“Sauran kuma, kamar kowannenmu na da irin gudunmawar da zai bayar a sabuwar gwamantin wajen farfado da al’amura da kuma ceto Najeriya.

“Sannan yana da mataimaki wanda matsashi ne mara tabo a bangaren nasarorin da ya samu a rauyuwa, da kuma harkokin jama’a,” in ji sakon na Obasanjo.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...