Search This Blog

Showing posts with label Kotun Tafi da Gidanka. Show all posts
Showing posts with label Kotun Tafi da Gidanka. Show all posts

Friday, 2 June 2023

Gwamnatin Kano Ta Kafa Kotunan Tafi Da Gidanka Domin Magance Satar Waya

Gwamnan jihar Kano, Yusuf Abba, ya amince da kafa kotunan tafi da gidanka domin tabbatar da hukunta masu satar wayar a jihar cikin gaggawa.


A wata sanarwa da sakataren yada labaran sa, Alhaji Bature Tofa ya fitar, ya ce kotunan tafi da gidanka za su hada hannu da rundunar hadin gwiwa ta musamman domin hukunta wadanda aka kama.

Yusuf ya ce manyan titunan birnin sun haska ne bayan shafe shekaru takwas na duhu yayin da aka kashe fitulun.

“Mayar da fitilun kan titi na cikin kokarin da sabuwar gwamnati ke yi na magance matsalar fashi da makami da sace-sacen waya da sauran miyagun ayyuka, musamman a babban birnin Kano.

"Aikin da ake ci gaba da gudanarwa ya fara tun ranar Talata kuma zai ci gaba har sai an kubutar da kowane bangare na jihar daga duhun da ke ba da mafaka ga masu aikata laifuka da 'yan bangar siyasa," in ji shi.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Head of Service Urges Civil Servants to Uphold Ethical Conduct

The Head of Service, Kano State, has called on civil servants to strictly adhere to the Civil Service ethical code and show grea...