Posts

Showing posts with the label Dan Majalisar Tarayya

Ayyukan Da Zan Yi Wa Al'umar Mazabata Cikin Shekarar 2024 - Abdulmumin Jibrin Kofa

Image
Bayan rantsar da ni a matsayin ɗan Majalisar Wakilai mai wakiltar mazaɓar Kiru/Bebeji, na yi hoɓɓasar ganin na kawo ayyukan raya ƙasa da ci gaban yankina. Kamar yadda buƙatun ainihin aikin da aka zaɓe ni don shi suke, na duƙufa ba dare ba rana wajen yin bincike domin gabatar da ƙudurorin da zan gabatar a zauren majalisa a ’yan watanni masu zuwa, waɗanda za su amfani ’yan mazaɓata da ma ƙasa baki ɗaya. A sakamakon haka, na tattauna da shugabannin kwamitoci daban-daban a Majalisa, na kuma rubuta wasiƙun neman ayyuka masu yawa da za aiwatar a mazaɓata a 2024, ƙari a kan wasu da zan yi da aljuhuna, kamar yadda na saba yi a baya. Yana da muhimmanci a fahimci cewa idan ban da aikin tituna (waɗanda na saka a kasafin kudin 2016, amma ba a aiwatar da su ba), na kawo ayyukan raya kasa masu tarin yawa a mazaɓata, na samar da gurabun ayyukan yi ga mutanen mazaɓata a hukumomi da ma’aikatun gwamnati masu yawa da kuma wasu hukumomin tsaro, duk waɗannan za a iya zuwa a tantance su.  Duka w

Kotun Sauraron Karar Zaben 'Yan Majalisa A Kano Ta Soke Zaben Dan Majalisar Tarayya Na NNPP

Image
Kotun sauraren kararrakin zabe ta Majalisar Dokoki ta Kasa da ta Jiha a Jihar Kano ta soke zaben Yusuf Umar Datti, dan takarar jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP) na mazabar Kura/Madobi/Garun Malam. Kotun da ke karkashin Mai shari’a Flora Ngozi Azingbe, ta yi watsi da zaben Yusuf saboda rashin yin murabus daga aikin koyarwa a Jami’ar Bayero ta Kano, cikin kwanaki 30 kafin zaben. Mai shari’a Azingbe ya kuma ce Datti ba zai iya gamsar da kotun ba cewa shi dan jam’iyyar NNPP ne. Bayan yanke hukuncin, Mai shari’a Azinge ya umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa da ta ajiye takardar shaidar cin zabe da aka baiwa Datti a baya tare da bayyana Musa Ilyasu Kwankwaso na jam’iyyar APC a matsayin wanda ya cancanta ya lashe zaben. Kwankwaso ya samu kuri’u mafi girma na biyu a zaben da aka gudanar a ranar 25 ga Fabrairu, 2023. A martanin da kotun ta yanke, Kwankwaso ya bayyana godiya da jajircewarsa wajen yi wa jama’a hidima, inda ya ce, “Na yaba da bangaren shari’a kan yadda