Posts

Showing posts with the label Kudin makaranta

Sanatan Kano Ya Ba Dalibai 620 Tallafin Karatu A BUK

Image
  Mataimakin Shugaban Majalisar Dattawa kuma Sanatan Kano ta Arewa Barau Jibrin ya ba wa daliban mazabarsa 628 tallafin karatu a Jami’ar Bayero ta Kano (BUK). Aminiya ta gano cewa duk dalibin mazabar da ya rabauta ya samu tallafin N50,000 daga dan majalisar. Da yake bude rabon tallafin, shugaban ma’aikatan Sanata Barau, Farfesa Muhammad Ibn Abdullahi, ya ce dan majalisar ya yi haka ne domin ba wa daliban mazabarsa damar neman ilimi a manyan makarantu. Kakakin Mataimakin Shugaban Majalisar, Ismail Mudashir, ya ce daliban mazabar Kano ta Arewa da ke sauran manyan makarantu a fadin Najeriya ma za su amfana da tallafin. Don haka ya bukaci daliban da suka amfana da su yi amfani da abin da aka ba su ta hanyar da ta dace sanna su kara jajircewa wajen neman ilimi. Wani dalibin aji hudu a jami’a da ya samu tallafin , Adama Iliyasu Rabiu, ya yaba wa dan dan majalisar tare da rokon Allah Ya saka masa. (AMINIYA)

Yanzu-Yanzu : Gwamnatin Kano Ta Sanar Da Rage Kashi Hamsin Cikin Dari Na Kudin Da Daliban Manyan Makarantu Ke Biya

Image
Gwamna Abba Kabir ne ya sanar da hakan a yammacin ranar Litinin Gwamnan yace ya bawa Shugabannin makarantun gaba da Sakandire dake Kano umarnin rage kudin da dalibai ke biya daga kaso dari zuwa kaso hamsin Alhaji Abba Kabir Yusuf wanda ya sanar da hakan ta shafinsa na Facebook, ya ce wannan mataki ya faru ne sakamakon tsananin rayuwa da jama’a ke fuskanta a halin yanzu a kasar nan 

Gwamnan Kano Zai Biya Wa Daliban BUK 7,000 Kudin Makaranta

Image
Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya bayar da umarnin biya wa daliban da ke karatu a Jami’ar Bayero (BUK) kimanin su 7,000 ’yan asalin Jihar kudin makaranta. Babban mai taimaka wa Gwamnan a kan harkokin kafafen sadarwa na zamani, Salisu Yahaya Hotoro, ne ya tabbatar da haka a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook da maraicen Laraba. “Gwamnan Jihar Kano, Engr. Abba Kabir Yusuf ya bayar da umarnin biya wa É—aliban jihar Kano da ke karatu a BUK su kimanin dubu bakwai kuÉ—in makaranta,” kamar yadda ya wallafa. Hakan na zuwa ne dai a daidai lokacin da daliban jami’ar ke ci gaba da kokawa da karin kudin da jami’ar ta yi. A sakamakon karin, dalibai da dama sun rika neman gwamnati da masu hannu da shuni da su tallafa musu. Hatta jami’ar ta Bayero sai da ta tsawaita wa’adin lokacin yin rajistar dalibai, kasancewar da dama daga cikinsu ba su iya kammalawa ba, saboda tsadar. (AMINIYA)

Muna buƙatar Buhari ya sa baki kan ƙarin kuɗin makaranta - Kungiyar Dalibai

Image
Ƙungiyar Ɗalibai ta Najeriya NANS ta buƙaci shugaban ƙasar Muhammadu Buhari ya yi ''gaggawar sa baki'' game da ƙarin kuɗin makaranta da jami'o'in ƙasar ke shirin yi tun kafin hakan ya janyo matsaloli a faɗin ƙasar''. Sakataren ƙungiyar na ƙasa Usman Baba Kankia, ya shaida wa BBC cewa ''duk makarantun gwamnatin tarayya sun ƙaƙƙara kuɗaɗe fiye da kashi 250 cikin dari'', A baya-bayan nan dai an ga yadda wasu daga cikin jami'o'in ƙasar suka bayyana ƙarin kuɗin makaranta. To sai dai Sakataren ƙungiyar ya ce suna zargin cewa makarantun sun samu umarnin ƙara kuɗin makarantar ne daga sama. Dalilin ya da sa kenan suka rubuta wasika ga shugaba ƙasa, inda suka buƙace shi a matsayinsa na uba, ya sa baki domin mayar da kuɗin makarantar yadda yake a baya. Wasu jami'o'in dai sun bayyana cewa sun yi ƙarin kuɗin makarantar ne domin samun damar gudanar da makarantun nasu. dalibai othersCopyright: others To sai dai ƙu