Posts

Showing posts with the label Kwamitin bincike

Kwamitin Binciken Kwato Kadarorin Gwamnati nlNa Jihar Kano Zai Gudanar Da Zama Ranar Litinin Mai Zuwa

Image
Kwamitin shari’a na binciken kadarorin gwamnati da Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya kafa domin binciken gwamnatin da ta gabata karkashin jagorancin tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya shirya gudanar da zamansa na farko a ranar Litinin 29 ga Afrilu, 2024. Sakataren kwamitin Salisu Mustapha ne ya bayyana hakan a wata wasika da ya aikewa mai magana da yawun Gwamnan Kano a ranar Asabar. Mustapha ya bayyana cewa zaman zai gudana ne a babbar kotu mai lamba 3 dake cikin sakatariyar Audu Bako a ranar Litinin 29 ga Afrilu, 2024 da karfe 10 na safe. A farkon wannan watan ne Gwamna Yusuf ya kaddamar da wasu kwamitocin bincike na shari’a guda biyu (JCI) domin binciken almubazzaranci da dukiyar jama’a da tashe-tashen hankulan siyasa da kuma bacewar mutanen da suka yi a tsakanin shekarar 2015 zuwa 2023. A yayin kaddamar da mambobin kwamitin, Gwamna Yusuf ya yi alkawarin hukunta duk wanda aka samu da laifi, inda ya jaddada kudirinsa na bankado tare da gurfanar da wadanda suka

Ganduje Yayi Kira Ga Gwamnatin Kano Ta Mayar Da Hankali Kan Kawo Ayyukan Ci Gaba Ba Wai Bata Sunan Wani Ba

Image
Shugaban jam’iyyar APC mai mulki ta kasa, Dakta Abdullahi Umar Ganduje, ya ja kunnen gwamna Abba Yusuf na jihar Kano da ya daina amfani da dabarun karkatar hankalin da jama’a wajen fakewa da gazawar sa ga al’ummar jihar. A sanarwar da babban sakataren yada labaran Shugaban APC na kasa, Edwin Olofu ya sanyawa hannu, yace Ganduje, a wata sanarwa da ya fitar ta hannun babban sakataren yada labaran sa, Edwin Olofu, ya bayyana irin halin da gwamnan ke ciki na baya-bayan nan a matsayin wani abin takaici da takaicin yunkurin karkatar da hankulan jama’a kan cewa a gaskiya babu wani abu a jihar da zai tabbatar da karin girma da aka samu a jihar. A cikin kason da doka ta tanada ga jihar tun lokacin da shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya jagoranci gwamnati a ranar 29 ga Mayu, 2023. Gwamna Ganduje na mayar da martani ne kan matakin da gwamnatin jihar Kano ta dauka na gurfanar da shi a gaban kotu bisa zarginsa da karbar cin hancin dala 413,000, da kuma Naira biliyan 1.38. Ganduje ya ce s

Gwamna Yusuf Ya Kaddamar da Kwamitocin bincike kan Tashe-tashen hankulan Siyasa da almubazzaranci da dukiyar al'umma.

Image
Gwamnan jihar Kano Alh. Abba Kabir Yusuf ya kaddamar da kwamitocin shari’a guda biyu na binciken shari’o’in almubazzaranci da dukiyar jama’a, tashe-tashen hankulan siyasa da kuma bacewar mutanen tsakanin 2015 zuwa 2023. Da yake kaddamar da mambobin kwamitocin a ranar Alhamis, Gwamna Yusuf ya sha alwashin gurfanar da duk wanda aka samu da laifi. A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun Gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, Gwamnan ya tunatar da cewa binciken almubazzaranci da dukiyar al’umma na daga cikin alkawarin da ya dauka na kaddamar da bincike tare da hukunta wadanda ke da hannu a rikicin siyasa da aka samu a jihar. Ya ce, "Tashin hankalin siyasa wani babban koma baya ne ga tsarin dimokuradiyya a duniya. Yana haifar da asarar rayuka da dukiyoyi da kuma rashin amincewa da jama'a da masu rike da madafun iko". "Bai kamata a share al'amuran kashe-kashen siyasa masu tayar da hankali ba musamman a shekarar 2023 su tafi kawai ba, don tabbatar