Posts

Showing posts with the label Yobe Ta Arewa

Kotun Koli Ta Tabbatar Da Ahmed Lawan A Matsayin Dan Takarar Sanata Na Yobe Ta Arewa

Image
Kotun koli a ranar Litinin ta tabbatar da Ahmed Lawan, shugaban majalisar dattawa a matsayin dan takarar sanata na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) a jihar Yobe ta arewa. A wani hukunci mafi rinjaye da mai shari’a Centus Nweze ya yanke, kotun kolin ta amince da daukaka karar da jam’iyyar APC ta shigar kan takarar Bashir Machina. Hukuncin da mafi rinjayen alkalai uku suka yanke wa 2, ya yi watsi da hukuncin da kotun daukaka kara ta Abuja ta yanke a ranar 28 ga watan Nuwamba, 2022, ta tabbatar da Bashir Sherrif Machina a matsayin dan takarar sanata na jam’iyyar APC na jihar Yobe ta Arewa a zabe mai zuwa. Sai dai mai shari’a Adamu Jauro da Emma Agim sun nuna rashin amincewa da hukuncin da aka yanke, wanda hakan ya sanya suka yanke hukuncin watsi da karar da jam’iyyar APC ta shigar tare da tabbatar da sakamakon binciken da kotunan da ta shigar da kara suka yi. Kamfanin dillancin labaran Najeriya ya ruwaito cewa Mai shari’a Monica Dongban-Mensen, wacce ta jagoranci kwam