Search This Blog

Showing posts with label Tafiya. Show all posts
Showing posts with label Tafiya. Show all posts

Wednesday, 10 May 2023

Gamu Da Tafiya A Motar Haya Kashi Na 4- Dr Dukawa

HALIN DA TITUNAN NAJERIYA SUKE CIKI
Tafiyar da muka yi daga Kano zuwa Yola ta dauke mu kimanin awa tara (9.30 na safe – 6.30 na yamma). Kuma na yaba da tukin direbanmu, wani matashi mai suna Uzairu dan kimanin shekara 25/6. Wannan tafiyar ta tuna min da wani majigi da shahararren masanin kimiyar siyasa, Farfesa Ali Mazrui, ya yi a shekarun 1980. Ali Mazrui dan asalin Kenya ne, ya auri ‘yar Najeriya, sun rayu a America har rasuwarsa. 

Guda daga cikin hanyoyin da Ali Mazrui ya bi wajen nuna tazarar da take tsaknin manyan kasashe da masu tasowa shine yadda ya dauko hoton wani titi a wata babbar kasa (watakil America) da motoci suna gudu kowacce a layinta. Sai ya ce: “duk wanda ka gani yana tuki yana kwane-kwane anan, to a cikin maye yake”. Sai kuma ya dauko wani titi na wata kasar mai tasowa (watakila Kenya ko Najeriya), da motoci suna ta kwane-kwane suna kaucewa ramukan kan titi. Sai ya ce: “anan kuma, duk wanda ka gani yana tafiya sambel babu kwane-kwane to a buge yake!” 

Yau kimanin shekara arba’in da wannan majigin na Ali Mazrui amman har yau titinan Najeriya sai ana tafiya ana ta kwane-kwane a wurare da yawa. Ga arziki Allah yana ta dada tuttudowa kasar amman lafiyayyun hanyoyin mota sun gagara. Illolin rashin hanya mai kyau suna da yawa. Ko ba a yi hatsari an rasa rayuka da dukiya ba fargabar yiwar afkuwar hakan ta ishi matafiya. Ga kuma saurin lallacewar abin hawa. 

Sai dai ko babu komai na lura gwamnatocin jihohin Adamawa da Taraba sun kokarta wajen samar da titinan cikin gari da magudanan ruwa masu kyau. Amman fa akwai tarin shara da ta rufe magudanan ruwa masu yawa. Yana da matukar muhimmanci gwamnatocinmu su samo kan yadda za a yi da shara a birananmu. Sannan akwai bukatar ko hadin guiwa ne su yi wajen gyara manyan titina idan gyaran ya gagari gwamnatin tarayya.

Tuesday, 9 May 2023

Game Da Tafiya A Motar Haya Kashi Na 3 - Dr Dukawa


HALIN DA WASU TASHOSHIN MOTA SUKE CIKI 

A bisa kiyasi, tashar Na’ibawa a Kano ba za ta gaza shekara arba’in (40) ba. Saboda an samar da ita ne a zamanin marigayi gwamnan tsohuwar jihar Kano Alhaji Abubakar Rimi (1979 – 1983). Amman har izuwa yau tashar tananan jiya ya yau: kango wanda babu wani abu da yake nuna ana samun kudi a wurin; babu kwalta, babu interlocks, babu dabe kowane iri! Zaiyar kasa. Sai yalwar leda da sauran nau’i na shara. Babu wani lafiyayyen makewayi. Da na bukaci wurin yin bawali sai aka nuna min wani uban juji a yammacin cikin tashar. Sai da roki wani dan bola jari cewar ya dan kauce zan kama ruwa. 

Na tabbatar idan ruwa ya sauka mummunan halin da tashar ke ciki ba zai gaza na tashar Unguwa Uku ta Kano ba, wacce na yi rubutu akan nata halin da take ciki a sherarar 2020. 

An yayyanka pilotai a cikin tashar Na’ibawa. Wasu an gina shaguna ana gudanar da ciniki wasu kuma an saka fandisho na gini ba a yi ginin ba. Babu Masallaci sai ‘yar musalla amman har da lasifika. Ko yaya aka yi a kasar Musulmi irin Kano za a yi tashar mota ta shekara arba’in ba a samar da masallaci ba sai abin ya daurewa mutum kai. Alhali ya kamata ace izuwa yanzu har dakin shan magani, da karamin dakin ATM da ofishin aika sako (akwatin gidan waya) na gaggawa, da kuma ofishin ‘yansanda ya kamata ace an samu.

Halin da na samu tashar mota a Yola da Jalingo bai sha banban da yadda na baro a Kano ba. Babu wani abu na cigaba. Sai turbaya da shara da bola.
Anan zan nanata kirana ga kananan hukumomi (LGAs) a Arewacin Najeriya cewar su tuna amanar da suka dauka na gudanar da ayyukan da aka zayyana a makale na hudu (fourth schedule) na Tsarin Mulkin Najajeriya. Daga ayyukansu akwai samarwa da kula da tashoshin mota. Wannan ba ya nufin a shata kango motoci su rika shiga suna lodi ‘yan rabanu (masu karbar kudin shiga) kuma suna karbar haraji kawai ba. 

Amman yana nufin a inganta tashoshi ta hanyar samar da yanayi mai kyau da tsabta da tsaro. Kunyoyin da suke karbar nasu kason a wurin direbobi su ma su sani cewar babban aikinsu shine su inganta sana’ar ta hanyar bibiyar hukumomi da neman su sauke nauyinsu da kuma taya hukumomin samar da wasu abubuwan inganta rayuwa a wurin sana’a. sabanin haka za su rika cin haram ne na wannan kudaden da suke karba.

Monday, 8 May 2023

Game Da Tafiya A Motar Haya Kashi Na Biyu


 


Daga Dr Sa'idu Ahmad Dukawa

TSARIN DAUKAR FASINJA A TASHA

Bayan da na yi tambayi game da tsarin daukar fasinja a tashar mota, na sami bayanin cewa mutum zai iya zuwa tsahar Na’ibawa (wacce a yanzu aka sakawa suna “tashar Kano Line”) ya yi booking (biyan kudi kafin ranar tafiya). Don haka sai na je ofishin Adamawa Sunshine (wanda alal hakika shago ne a cikin tashar da dan teburi da mutumin da yake karbar kudi ya rubuta rasiti), na biya kudina ana kashegarin ranar tafiya.

Na tambaya mutum nawa ake dauka a mota kirar sienna? Aka ce min ana daukar mutum takwas ne, fasinja biyu a gaba, uku a tsakiya, uku a karshe. Amman fa Bature ya yi motar ne domin daukar fasinja biyar: guda a gaba, biyu a tsakiya, biyu a karshe. Don haka ana wuce kima (overload) na mutum uku. A motar ‘yankasuwa kuwa har mutum hudu ake sakawa a tsakiya, kamar yadda na ganewa idona a yayin dawowata daga Jalingo zuwa Kano. Allah ya kiyaye, a duk lokacin da aka gamu da hadari, za ta yiwu a yi asarar rayuka tara zuwa goma a cikin mota guda. A inda aka san kimar rai, duk yadda za a yi a rage asarar rai guda ana yi.

Ko me yasa dole sai an yi overload a motocin haya a Najeriya? Dalilan sanannu ne. farko dai akwai tsadar man fetur. Na biyu akwai biyan haraji hawan hawa, hukuma ta karba, kungiyoyi su amsa, yan kamasho su yaga, a dankawa ‘yan wururu masu taro fasinja daga hanya su kawo shi gindin mota, a dankawa masu gadin tasha, a yi ta mikawa jami’an tsaro kashi kashi (na kidaya shingen jami’an tsaro kimanin dozen guda a tsaknin Jalingo da Gombe kadai). Ga kuma tsadar kayan mota (spare parts) tunda kusan komai sai an yi odarshi, ba a kera komai a kasar. Ga mamallakin mota yana so ya mayar da kudinsa da wuri, don haka yana son a rika kawo balance mai tsoka a duk rana.

A karshe ga bukatar Direban motar na ya samu abinda zai shiga gida da shi ya sallami iyali. Idan aka hada duk wadannan bukatun akan fasinja kuma ba zai iya dauka ba. Don haka akan dole ake gwammacewa a cunkusa fasinja, wani a jikin wani, kamar kifin sardine.

Akwai kuma abinda yake ya shafi dabi’a ta rashin tsari da ci da zuci da rashin ganin kimar dan Adam wacce take tattare da mutane da yawa, barin idan sun san babu wata doka za ta hau kansu. Alal misali, na biya kudin kujera uku na tsakiya yayin da zan tafi, saboda tare da iyali zan yi tafiyar.

Amman ko da muka zo tasha sai muka taras an cushe wurin ajiyar kaya, babu inda zamu saka ‘yan kananan jakunkunanmu kwara biyu, wadanda idan mun yi tafiya a jirgin sama ba ma auna su, da su muke shiga jirgi, saboda karancin girma ko nauyi da suke da shi. Sai aka nemi wai tunda mu biyu ne kacal a tsakiya, wurin zai ishemu har kayanmu. Ni kuma nace ban amince ba. Daga dukkan alamu kuma sun riga sun sayar da wurin ajiyar kayana, sun karbi sakon kaya wanda shima na samu labarin kudin kujera ake biyansu. Na duba rasitin da aka bani ko akwai lambar wayar ofis sai na kai korafi sai naga in banda sunan na “Adamawa Sunshine” babu komai a jiki, babu lambar waya, babu adireshi! A karshe dai sai saukemu aka yi daga motar, ni da iyalina, na jira wata ta yi lodi bayan sa’a uku, sannan muka kama hanya.

A nan akwai bukatar ace daga cikin jerin masu karbar kudin shiga akwai wadanda suke sa ido wajen ganin an bi ka’ida, an cika alkawari, ko Allah ya sa albarka a harkar da kuma a rayuwarmu baki daya. Wasu shawarwarin da za su biyo baya da za su karfafi wannan, da yardar Allah.

Saturday, 6 May 2023

Game Da Tafiya Da Motar Haya A Najeriya Kashi Na Daya

Daga 
Dr. Saidu Ahmad Dukawa

SHIMFIDA
A ranar Talata, 25/4/2023, na shiga motar haya daga Kano zuwa Yola, babban birnin jihar Adamawa a Najeriya. Ranar Alhamis kuma, 27/4/23, na shiga wata motar hayar daga Yola zuwa Jalingo, babban birnin jihar Taraba. Rabona da tafiyar motar haya wacce ta kai tsawan haka tun a shekarun 1983 zuwa 1984 a yayin da na yi hidimar Kasa (NYSC) daga jihar Kano zuwa jihar Bauchi, sai kuma jihar Lagos da na je bayan kammala hidimar kasa a wajejen shekarar 1985.

A wannan karon ma tafiyar ta taso min ne a dalilin wata hidimar Kasar, watau aikin kula da yadda jarrabawar shiga jami’o’i ta kasa (UTME) take gudana. Tun daga lokacin da aka nada Farfesa Is’haq Oloyede a matsayin Magatakardar Hukuma mai tsarawa da gudanar da jarrabawa domin shiga jami’a a Najeriya (JAMB), a shekarar 2016, ya fitar da sababbin tsare-tsare na yadda ake gudanar da wannan jarrabawar. Daga ciki akwai samar da kwamitoci daban daban, har guda goma sha daya (11), domin gudanar da ayyuka daban daban. Guda daga cikin wadannan kwamitoci shine wanda aka lakabawa suna a Turance da “Roving Group”. Watau kwamiti mai kewayawa santocin da ake gudanar da jarrabawa domin kula da yadda jarrabawar take gudana da nufin gano al’amuran da suke bukatar daukar mataki na gaggawa da kuma wadanda za a zauna a tsanake, a yi musu tunani, a samar da yadda za a ingantasu a shekara mai zuwa. Na sami kaina a cikin wannan kwamiti, a inda na shekara biyu ina aiki a Abuja, shekara guda a Adamawa, shekara uku a Kano, bana kuma aka bukaci na je aiki a Adamawa da Taraba.

Abubuwa uku kwamitin da na yi bayaninsa aka dorawa nauyin kula da su, kamar haka:

1. Yanayin tsaro a ciki da kewayen wurin jarrabawa (CBT Centre); saboda Farfesa Oloyede ya karbi aiki a yayin da a ake cikin kamarin kalu-balen tsaro akasa, musamman na ‘yan Boko Haram;

2. Yanayin tantance dalibai masu zana jarrabawa; saboda amfani da fasahar zamani na tantance masu zana jarrabawa (biometrics) da aka shigo da shi; da kuma

3. Yanayin da dakunan da ake gudanar da jarrabawar suke ciki, da inganci da yalwar na’urori masu kwakwalwa (computers); saboda sababbin santoci masu zaman kansu da aka yiwa rajista ta gudanar da jarrabawar.

Amman fa ba akan wannan aikin zan yi bayani ba, saboda aiki ne da ya shafi hukuma, kuma duk wani bayani ita ake turawa ita kuma ta fitar da wanda ya shafi al’umma ta rike na rikewa. Na dan yi wannan tsokacin ne domin a san dan kadan daga irin hidimar da ake yiwa jarrabawa. Zan yi wannan dan takaitaccen rubutun ne akan abubuwa guda biyar:

1. Tsarin daukar fasinja a tasha
2. Halin da wasu tashoshin mota
 suke ciki

3. Halin da titunan Najeriya suke ciki a shekara ta 2023

4. Yanayin tuki da yanayin larurar bukata a yayin tafiya

5. Yanayin tsaro da alakar jami’an tsaro da direbobin mota.

Babban burina da wannan rubutun shine fata da nake da shi na ko Allah ya sa masu ruwa da tsaki su ci karo da rubutun kuma ya sa su inganta al’amura game da abinda ya shafi tafiya a motar haya a Najeriya.
Manya daga cikin masu ruwa da tsaki kuwa sun hada da Kananan Hukomomi (Local Government Authorities), Kungiyoyin sufuri, da na mamallaka motocin haya, da na direbobin haya, da na ‘yan kamasho, da kuma jami’an tsaro, da sauransu. Zan yi kokarin takaita bayani domin gudun kosarwa. Kuma zan raba posting din kashi kashi duk dai saboda gudun kosawa.

(Za a cigaba da magana akan Tsarin Daukar Fasinja a Tashar Mota, da yardar Allah) 

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...