Posts

Showing posts with the label Kadarorin gwamnati

Kwamitin Binciken Kwato Kadarorin Gwamnati nlNa Jihar Kano Zai Gudanar Da Zama Ranar Litinin Mai Zuwa

Image
Kwamitin shari’a na binciken kadarorin gwamnati da Gwamna Abba Kabir Yusuf na jihar Kano ya kafa domin binciken gwamnatin da ta gabata karkashin jagorancin tsohon Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya shirya gudanar da zamansa na farko a ranar Litinin 29 ga Afrilu, 2024. Sakataren kwamitin Salisu Mustapha ne ya bayyana hakan a wata wasika da ya aikewa mai magana da yawun Gwamnan Kano a ranar Asabar. Mustapha ya bayyana cewa zaman zai gudana ne a babbar kotu mai lamba 3 dake cikin sakatariyar Audu Bako a ranar Litinin 29 ga Afrilu, 2024 da karfe 10 na safe. A farkon wannan watan ne Gwamna Yusuf ya kaddamar da wasu kwamitocin bincike na shari’a guda biyu (JCI) domin binciken almubazzaranci da dukiyar jama’a da tashe-tashen hankulan siyasa da kuma bacewar mutanen da suka yi a tsakanin shekarar 2015 zuwa 2023. A yayin kaddamar da mambobin kwamitin, Gwamna Yusuf ya yi alkawarin hukunta duk wanda aka samu da laifi, inda ya jaddada kudirinsa na bankado tare da gurfanar da wadanda suka

El-Rufai Zai Rushe Kamfanoni 9 Mallakar Makarfi

Image
Gwamna Nasir El-Rufai na Jihar Kaduna, ya soke lasisin mallakar kamfanoni tara na tsohon gwamnan jihar, Sanata Ahmed Muhammed Makarfi. An kuma shirya rushe kamfanoni tara mallakar tsohon gwamnan Jihar. Aminiya  ta fahimci cewa an kai sanarwar janye  hakkin mallaka ga jami’an kamfanonin da abin ya shafa. Sanarwar ta fito ne daga Daraktan kamfanin rake da ke lamba 11 a Murtala Square, Alhaji Ibrahim Makarfi wanda ya mayar da martani da cewa, “lauyoyinmu za su mayar da martani kan kwace hakkin mallakar kamfanonin”. Sai dai da yake mayar da martani kan soke hakkin mallakar a wani sakon da ya aike wa Sanata Makarfi, ya tabbatar da samun wasikun soke kamfanonin har guda tara. Ya ce, “Akwai babban batu. Muna bukatar ganawa da Ustaz Yunus (SAN) domin mu garzaya kotu don dakatar da gwamnatin jiha; kawai sun aiko mana da takardun soke mallaka guda tara”. Daga cikin kadarorin da abin ya shafa sun hada da filaye guda biyar a Mogadishu, filaye uku a kan titin Kwato, da fili daya a Doka.